< Isaïe 37 >

1 Lorsque le roi Ezéchias les eut entendus, il déchira ses vêtements, et, couvert d’un cilice, il se rendit dans la maison de Dieu.
Sa’ad da Sarki Hezekiya ya ji haka, sai ya kyakkece rigunansa ya kuma sanya tsummoki ya tafi ya shiga haikalin Ubangiji.
2 Puis il envoya Elyakim, l’intendant du palais, Chebna, le secrétaire, et les plus anciens des prêtres, enveloppés d’un cilice, auprès du prophète Isaïe, fils d’Amoç,
Ya aiki Eliyakim sarkin fada, Shebna magatakarda da kuma manyan firistoci, duka sanye da tsummoki, wurin Ishaya ɗan Amoz.
3 avec ce message: "Ainsi parle Ezéchias: C’Est aujourd’hui un jour d’angoisse, de châtiment et d’humiliation; les enfants sont près de naître, mais point de force pour enfanter!
Suka faɗa masa cewa, “Ga abin da Hezekiya ya ce wannan rana ce ta baƙin ciki da tsawatawa da shan kunya, sai ka ce sa’ad da’ya’ya kan zo matakin haihuwa sa’an nan a rasa ƙarfin haihuwarsu.
4 Peut-être l’Eternel, ton Dieu, accordera-t-il son attention aux paroles de Rabchakè, envoyé par le roi d’Assyrie pour outrager le Dieu vivant, et voudra-t-il demander compte de ces paroles qu’il a entendues. Prie donc en faveur des débris qui subsistent encore."
Mai yiwuwa Ubangiji Allahnka zai ji maganganun sarkin yaƙin da maigidansa, sarkin Assuriya, ya aika don yă zagi Allah mai rai, ya kuma tsawata masa saboda maganganun da Ubangiji Allahnka ya ji. Saboda haka ka yi addu’a saboda raguwar da suke da rai.”
5 Les serviteurs du roi Ezéchias se rendirent auprès d’Isaïe.
Sa’ad da shugabannin Sarki Hezekiya suka zo wurin Ishaya,
6 Celui-ci leur dit: "Vous parlerez ainsi à votre maître: Ne sois pas effrayé, a dit l’Eternel, des paroles que tu as entendues, des blasphèmes proférés contre moi par les jeunes gens du roi d’Assyrie.
sai Ishaya ya ce musu, “Ku faɗa wa maigidanku cewa, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa. Kada ka ji tsoron abin da ka ji, maganganun nan da bayin sarkin Assuriya suka yi mini saɓo.
7 Je lui inspirerai la résolution de retourner dans son pays à la suite d’une nouvelle qui lui parviendra; là, je le ferai périr par le glaive."
Ka saurara! Zan sa ruhuna a cikinsa saboda sa’ad da ya ji wani labari, zai koma zuwa ƙasarsa, a can kuwa zan sa a kashe shi da takobi.’”
8 Lorsque Rabchakè revint auprès du roi d’Assyrie, il le trouva aux prises avec Libna; il avait, en effet, appris son départ de Lakhich.
Sa’ad da sarkin yaƙin ya ji cewa sarkin Assuriya ya bar Lakish, sai ya janye ya kuma sami sarki yana yaƙi da Libna.
9 Or, le roi d’Assyrie reçut l’information suivante: "Tirhaka, roi d’Ethiopie, marche contre toi pour te combattre." À cette nouvelle, il envoya des messagers auprès d’Ezéchias avec cet ordre:
To, fa, Sennakerib ya sami labari cewa Tirhaka, mutumin Kush sarkin Masar, yana fitowa don yă yi yaƙi da shi. Sa’ad da ya ji haka, sai ya aiki jakadu zuwa wurin Hezekiya da wannan magana.
10 Vous parlerez à Ezéchias, roi de Juda, en ces termes: "Ne te laisse pas leurrer par ton Dieu, en qui tu mets ta confiance, en te disant que Jérusalem ne tombera pas au pouvoir du roi d’Assyrie.
“Ku faɗa wa Hezekiya sarkin Yahuda cewa kada ka bar allahn da ka dogara a kai ya ruɗe ka sa’ad da ya ce, ‘Ba za a ba da Urushalima ga sarkin Assuriya ba.’
11 Certes, toi aussi tu as appris les exploits accomplis par les rois d’Assyrie dans tous les pays qu’ils ont dévastés. Et toi, tu serais sauvé!
Tabbatacce ka ji abin da sarakunan Assuriya suka aikata ga dukan ƙasashe, suna hallaka su tas. Kai kuwa za ka tsira ne?
12 Les dieux ont-ils pu assurer le salut des peuplades que mes ancêtres ont anéanties: Gozân et Haran, Récéf et les Benê-Eden établis à Telassar?
Allolin al’umman da kakannina suka hallaka sun cece su ne, allolin Gozan, Haran, Rezef da kuma na mutanen Eden waɗanda suke zama a Tel Assar?
13 Où est le roi de Hamat, le roi d’Arpad, le roi de Laïr, Sefarvayim, Hèna et Ivva?"
Ina sarkin Hamat yake, sarkin Arfad fa, sarkin Sefarfayim, ko na Hena ko na Iffa?”
14 Ezéchias prit la lettre de la main des messagers et, après l’avoir lue, il se rendit dans la maison de Dieu et déploya cette lettre devant l’Eternel.
Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga jakadun ya karanta ta. Sa’an nan ya haura zuwa haikalin Ubangiji ya shimfiɗa ta a gaban Ubangiji.
15 Puis Ezéchias adressa la prière suivante à l’Eternel:
Sai Hezekiya ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
16 "Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël, toi qui trônes sur les chérubins, tu es le seul Dieu de tous les royaumes de l’univers, c’est toi qui as créé le ciel et la terre.
“Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, zaune a tsakanin kerubobi, kai kaɗai ne Allah a kan dukan masarautan duniya.
17 Seigneur, prête l’oreille et écoute, ouvre les yeux et regarde! Accorde ton attention au message envoyé par Sennachérib pour blasphémer le Dieu vivant!
Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka kuma ji; ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka kuma gani; ka saurara ga dukan maganganun da Sennakerib ya aika don yă zagi Allah mai rai.
18 II est vrai, Eternel, que les rois d’Assyrie ont ruiné tous les peuples avec leurs territoires,
“Gaskiya ce, ya Ubangiji, cewa sarakunan Assuriyawa sun mai da dukan waɗannan mutane da ƙasashensu kango.
19 et livré leurs divinités aux flammes. Mais ce n’étaient point des dieux, c’étaient des œuvres fabriquées par l’homme, du bois et de la pierre; on les a donc anéanties.
Sun jefar da gumakansu cikin wuta suka kuma hallaka su, gama su ba alloli ba ne itace ne kawai da dutse, da hannuwan mutane suka sarrafa.
20 Et maintenant, protège-nous contre lui, Eternel, notre Dieu, afin que tous les royaumes de la terre reconnaissent que seul, ô Seigneur, tu es Dieu."
Yanzu, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga hannunsa, saboda masarautai a duniya su san cewa kai kaɗai ne, ya Ubangiji, Allah.”
21 Isaïe, fils d’Amoç, manda à Ezéchias: "Ainsi parle l’Eternel, le Dieu d’Israël: En raison de la prière que tu m’as adressée à cause de Sennachérib, roi d’Assyrie,
Sa’an nan Ishaya ɗan Amoz ya aika da saƙo wa Hezekiya cewa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa. Saboda ka yi addu’a gare ni game da Sennakerib sarkin Assuriya,
22 voici l’oracle prononcé sur lui par l’Eternel: "Elle te dédaigne, se rit de toi, la vierge, fille de Sion; elle hoche la tête après toi, la fille de Jérusalem.
ga abin da maganar Ubangiji ya faɗa a kansa, “Budurwa Diyar Sihiyona ta rena tana kuma maka ba’a. Diyar Urushalima tana kada kai yayinda kake gudu.
23 À qui vont tes blasphèmes et insultes? Contre qui élèves-tu la voix? Tu as porté haut tes regards contre le Saint d’Israël.
Wane ne ka zargi ka kuma yi wa saɓo? A kan wa ka tā da muryarka ka kuma daga idanu cikin fariya? A kan Mai Tsarkin nan na Isra’ila!
24 Par tes émissaires, tu as outragé Dieu; tu as dit: "Avec mes nombreux chars j’ai escaladé la cime des montagnes, les pentes escarpées du Liban; j’abats ses cèdres superbes, ses plus beaux cyprès; j’atteins le gîte de son dernier sommet, ses taillis les plus touffus.
Ta wurin jakadunka ka jibge zage-zage a kan Ubangiji. Ka kuma ce, ‘Da kekunan yaƙina masu yawa na hau ƙwanƙolin duwatsu, ƙwanƙolin mafi tsayi na Lebanon. Na sassare al’ul mafi tsayi fir mafi kyau. Na kai can wuri mafi nisa na kurminsa.
25 J’Ai fait jaillir des sources, et j’ai bu leurs eaux. Sous la plante de mes pieds je mets à sec tous les canaux de l’Egypte."
Na haƙa rijiyoyi a baƙuwar ƙasa na kuma sha ruwa a can. Da tafin ƙafafuna na busar da dukan rafuffukan Masar.’
26 N’As-tu pas compris que j’ai tout résolu de loin, préparé ces événements dès les temps antiques? Maintenant je les ai suscités, pour que, détruites par toi, des villes fortes se changent en monceaux de ruines.
“Ba ka ji ba cewa tun dā can na shirya ya zama haka? A kwanakin dā na kafa shi; yanzu na sa ya faru, cewa ka mai da birane masu mafaka zuwa tsibin ɓuraguzai.
27 Leurs habitants, réduits à l’impuissance, ont été frappés de terreur et de confusion, semblables à l’herbe des champs, au vert gazon, à la mousse des toits et au blé flétri avant de monter en épis.
Mutanensu, suka rasa ƙarfi, sun firgita suka kuma sha kunya. Suka zama kamar tsire-tsire a gona, kamar tsire-tsiren ta suka tohu, kamar ciyawar da ya tsiro a kan rufi, wadda zafi ya yi wa ƙuna kafin tă yi girma.
28 Que tu demeures chez toi, que tu entreprennes des expéditions, je le sais, comme je connais tes emportements contre moi.
“Amma na san inda kake zama da sa’ad da kakan fita ka kuma koma da yadda ka harzuƙa gāba da ni.
29 Puisque tu t’emportes contre moi, et que tes discours arrogants sont montés à mes oreilles, je fixerai mon anneau à ton nez et mon mors entre tes lèvres, et te ferai reprendre le chemin par où tu es venu."
Saboda ka harzuƙa gāba da ni kuma saboda girmankanka ya kai kunnuwana, zan sa ƙugiya a hancinka linzamina a bakinka, zan kuma sa ka koma ta hanyar da ka zo.
30 Et ceci te servira de signe: cette année on mangera le produit spontané des champs, la seconde année ce qui repoussera encore de soi-même, mais la troisième année, vous ferez des semailles et des récoltes, vous planterez des vignes et en consommerez le produit.
“Wannan zai zama alama gare ka, ya Hezekiya, “Wannan shekara za ka ci abin da ya yi girma da kansa, shekara ta biyu kuma abin da ya tsiro daga wancan. Amma a shekara ta uku za ka yi shuki ka kuma girba, za ka dasa gonakin inabi ka kuma ci’ya’yansu.
31 Les débris qui ont survécu de la maison de Juda étendront de nouvelles racines sous la terre et porteront des fruits au-dessus.
Sauran da suka rage na gidan Yahuda kuwa za su yi saiwa a ƙarƙashi su kuma ba da’ya’ya a bisa.
32 Oui, un reste refleurira à Jérusalem et des débris sur la montagne de Sion; voilà ce que réalisera l’amour de l’Eternel-Cebaot.
Gama daga Urushalima raguwa za tă fito, kuma daga Dutsen Sihiyona ƙungiyar waɗanda suka tsira. Himmar Ubangiji Maɗaukaki zai cika wannan.
33 Aussi l’Eternel a-t-il fait cette déclaration au sujet du roi d’Assyrie: Il ne pénétrera pas dans cette ville, n’y lancera aucune flèche, ne lui opposera pas un seul bouclier, et n’établira pas de redoute contre elle.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarkin Assuriya, “Ba zai shiga wannan birni ba ya harbe kibiya a nan. Ba zai zo gabansa da garkuwa ba ko ya gina mahaurai kewaye a kansa ba.
34 Il reprendra le chemin par où il est venu, mais dans cette ville (dit l’Eternel) il n’entrera pas.
Ta hanyar da ya zo da ita zai koma; ba zai shiga wannan birni ba,” in ji Ubangiji.
35 Car je la protégerai, cette ville, pour son salut, en faveur de moi et de mon serviteur David."
“Zan kāre wannan birni in kuma cece shi, saboda girmana da kuma saboda sunan Dawuda bawana!”
36 Un ange du Seigneur se rendit au camp assyrien et y fit périr cent quatre-vingt-cinq mille hommes; en se levant le matin, on aperçut tous ces cadavres.
Sai mala’ikan Ubangiji ya fita ya kuma karkashe mutane dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar a sansanin Assuriya. Sa’ad da mutane suka farka kashegari, sai ga gawawwaki duk a kwance!
37 Sennachérib, roi d’Assyrie, leva alors le camp, prit le chemin du retour et s’arrêta à Ninive.
Saboda haka Sennakerib sarkin Assuriya ya janye. Ya koma zuwa Ninebe ya zauna a can.
38 Là, pendant qu’il était prosterné dans le temple de son dieu Nisrokh, Adrammélec et Charécér, ses fils, le frappèrent de leur glaive, puis s’enfuirent dans le pays d’Ararat. Ce fut son fils Essar-Hadon qui lui succéda.
Wata rana, yayinda yake yin sujada a haikalin allahnsa Nisrok,’ya’yansa maza Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka kuma gudu zuwa ƙasar Ararat. Esar-Haddon ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.

< Isaïe 37 >