< Isaïe 32 >

1 Voilà qu’un roi régnera alors pour la justice et que des princes gouverneront pour le droit.
Duba, sarki zai yi mulki cikin adalci masu mulki kuma su yi mulki da adalci.
2 Ils seront tous comme un refuge contre le vent et un abri contre l’orage, comme des cours d’eau dans des lieux arides, comme l’ombre d’un rocher puissant sur un sol altéré.
Kowane mutum zai zama kamar wurin fakewa daga iska mafaka kuma daga hadari, kamar rafuffukan ruwa a hamada da kuma inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa.
3 Ceux qui voient n’auront plus les yeux troubles, ceux qui entendent prêteront une oreille attentive.
Sa’an nan idanun waɗanda suka gani ba za su ƙara rufewa ba, kunnuwan waɗanda suka ji kuma za su saurara.
4 L’Intelligence des gens légers apprendra à connaître, et la langue des bègues s’exprimera avec facilité et clarté.
Zuciya marasa haƙuri za su sani su kuma fahimta, harshen masu ana’ana kuma zai sāke su yi magana sosai.
5 L’Homme pervers ne sera plus qualifié de noble et le fourbe ne passera plus pour généreux.
Ba za a ƙara ce da wawa mai girma ba ko kuwa a ɗaukaka mazambaci.
6 Car l’homme pervers débite des propos pervers, son cœur machine l’iniquité, pour accomplir des actions scélérates, proférer contre Dieu des faussetés, pour faire languir d’inanition celui qui a faim et priver de breuvage celui qui a soif.
Gama wawa maganar wauta yakan yi, zuciyarsa ta cika da mugunta, yana aikata abubuwan rashin sanin Allah yana baza kurakurai game da Ubangiji; yana barin mayunwata da yunwa ya kuma hana masu ƙishirwa ruwan sha.
7 Le fourbe, ses armes sont mauvaises; il trame des projets perfides, afin de perdre les pauvres par des paroles de mensonge et l’indigent qui réclame son droit.
Matakan mazambaci mugaye ne, yana ƙulla mugayen shirye-shirye don yă hallaka talakawa da ƙarairayi, ko sa’ad da roƙon mai bukata da gaskiya ne.
8 L’Homme généreux, lui, ne conçoit que des desseins généreux, et il persévère dans sa noblesse.
Amma mutumin kirki kan yi shirye-shirye masu kirki, kuma yakan tsaya a kan ayyukan kirki.
9 Femmes paisibles, levez-vous, entendez ma voix; et vous, filles insouciantes, écoutez mon discours.
Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ku tashi ku saurare ni; ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya, ku ji abin da zan faɗa!
10 Dans un an et des jours, vous serez troublées, vous qui vivez en pleine quiétude; car c’en est fini des vendanges, et de récolte, il n’en viendra plus.
Cikin ɗan lokaci ƙasa da shekara guda ku da kuke tsammani kuna da kāriya za ku yi rawar jiki; girbin’ya’yan inabi zai kāsa, girbin’ya’yan itatuwa kuma ba zai zo ba.
11 Prenez peur, femmes paisibles, tremblez, filles insouciantes; dépouillez vos vêtements, mettez-vous à nu, qu’un cilice couvre vos reins!
Ku yi rawar jiki, ku mata masu jin daɗi, ku sha wahala, ku’yan matan da kuke tsammani kuna da kāriya! Ku tuɓe rigunanku, ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku.
12 On se frappe la poitrine en pleurant les champs magnifiques, les vignes fertiles!
Ku bugi ƙirjinku don gonaki masu kyau don’ya’yan inabi
13 Sur le sol de mon peuple poussent les ronces et les épines: elles envahissent même les maisons de plaisance, la ville joyeuse.
da kuma don ƙasar mutanena, da ƙasar da ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suka yi girma, I, ku yi kuka saboda dukan gidajen da dā ake biki da kuma domin wannan birnin da dā ake murna a ciki.
14 Car les palais sont délaissés, la cité bruyante est dans l’abandon; tour et château-fort sont devenus en permanence des cavernes, la joie des onagres, un pâturage pour les troupeaux,
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
15 jusqu’au jour où se répandra sur nous un esprit d’en haut, où le désert redeviendra un verger et le verger sera considéré comme une forêt touffue.
sai an zubo Ruhu a kanmu daga sama, hamada kuma ta zama ƙasar mai taƙi, gona mai taƙi kuma ta zama kamar kurmi.
16 Alors le droit élira domicile dans le désert, et la justice aura son siège dans les jardins plantureux.
Aikin gaskiya zai zauna a hamada adalci kuma zai zauna a ƙasa mai taƙi.
17 Et l’œuvre de la justice sera la paix, et le fruit de la droiture sera le calme et la sécurité à tout jamais.
Aikin adalci zai zama salama; tasirin adalci zai zama natsuwa da tabbaci har abada.
18 Mon peuple habitera dans un séjour de paix, dans des demeures bien protégées et dans des retraites tranquilles.
Mutanena za su zauna lafiya a wuraren salama, a gidaje masu kāriya, a wuraren hutun da babu fitina.
19 Mais une grêle violente s’abattra sur la forêt, et la ville sera profondément abaissée.
Ko da yake ƙanƙara za tă fāɗo a jeji, a kuma rurrushe birni gaba ɗaya,
20 Heureux cependant, ô vous qui pourrez semer au bord de tous les cours d’eaux et laisser circuler librement le bœuf et l’âne!
zai zama muku da albarka, ku da kuke shuki iri kusa da kowane rafi, kuna kuma barin lafiyayyiyar makiyaya domin shanu da jakunanku.

< Isaïe 32 >