< Isaïe 25 >
1 Eternel, tu es mon Dieu! Je veux t’exalter et louer ton nom, car tu as accompli des merveilles, parfaitement fidèle aux résolutions prises dès longtemps.
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
2 Tu as fait de la ville un monceau de pierres, de la cité fortifiée un amas de ruines; la citadelle des barbares est rayée du nombre des villes, plus jamais elle ne sera rebâtie.
Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
3 C’Est pourquoi des peuples forts te révèrent, les cités de nations puissantes te craignent.
Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
4 Car tu as été un refuge pour l’humble, un refuge pour le pauvre en sa détresse, un abri contre l’averse, un ombrage contre la chaleur: le souffle des tyrans est comme l’averse battant les murs.
Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
5 Ainsi que fait la chaleur dans les régions arides, tu domptes l’arrogance des barbares; pareil à la chaleur qui passe par d’épais nuages, le chant triomphal des tyrans s’éteint.
kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
6 Et l’Eternel-Cebaot donnera à toutes les nations, sur cette montagne, un festin de mets succulents, un festin de vins de choix, de mets pleins de moëlle, de vins vieux clarifiés.
A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
7 Sur cette même montagne, il déchirera le voile qui enveloppe toutes les nations, la couverture qui s’étend sur tous les peuples.
A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
8 À jamais il anéantira la mort, et ainsi le Dieu éternel fera sécher les larmes sur tout visage et disparaître de toute la terre l’opprobre de son peuple: c’est l’Eternel qui a parlé.
zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
9 On dira en ce jour: "Voici notre Dieu en qui nous avons mis notre confiance pour être secourus, voici l’Eternel en qui nous espérions: soyons à la joie et à l’allégresse à cause de son appui."
A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
10 Car la main de l’Eternel se posera sur cette montagne, et Moab en sera écrasé dans son pays, comme la paille est écrasée dans la fosse à fumier.
Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
11 Dans cette fosse, Moab étendra les bras ainsi que fait le nageur pour nager, mais Dieu abattra son orgueil de même que les pièges dressés par ses mains.
Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
12 Tes remparts puissants et altiers, il les inclinera, les fera tomber et rouler à terre, en pleine poussière.
Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.