< Osée 2 >
1 Appelez vos frères Ammi ("mon peuple") et vos sœurs Rouhama ("chérie")!
“Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
2 Prenez-vous-en à votre mère, oui, prenez-vous-en à elle, si elle n’est plus ma compagne, si je ne suis plus son époux! Qu’elle bannisse de sa face la prostitution, de son sein l’adultère!
“Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
3 Sinon, je la dépouillerai de ses vêtements et la mettrai à nu comme au jour de sa naissance; et je la ferai semblable à un désert, je la rendrai comme un sol aride, et je la ferai périr de soif.
In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
4 Ses enfants, je n’en aurai point pitié, car ce sont les enfants de la débauche.
Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
5 Car elle est débauchée, leur mère, éhontée, celle qui les a conçus; car elle a dit: "Je m’attacherai aux pas de mes amants, qui me pourvoient de pain et d’eau, de laine et de lin, d’huile et de liqueurs."
Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
6 Eh bien! moi, j’embarrasserai son chemin de broussailles, j’y élèverai une clôture, et elle ne reconnaîtra plus ses sentiers.
Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
7 Elle courra après ses amants, elle ne pourra les atteindre; elle les cherchera, elle ne les trouvera point. Alors elle dira: "Allons, revenons à mon premier époux: j’étais jadis plus heureuse qu’aujourd’hui."
Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
8 Elle ne le savait donc pas, que c’est moi qui lui donnais le blé, et le vin et l’huile, qui lui prodiguais cet argent et cet or, dont on se servait en l’honneur de Baal!
Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
9 Aussi reprendrai-je mon blé en son temps et mon vin en sa saison; aussi lui arracherai-je ma laine et mon lin, qui recouvrent sa nudité.
“Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
10 Et ainsi j’étalerai son infamie aux regards de ses amants, et nul ne la sauvera de mon pouvoir.
Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
11 Je mettrai fin à toutes ses joies, à ses fêtes, ses néoménies, ses sabbats, à toutes ses solennités.
Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
12 Je dévasterai ses vignes et ses figuiers, "gages d’amour, disait-elle, que m’ont donnés mes adorateurs"; et j’en ferai un bois que ravagera la bête sauvage.
Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
13 Je lui ferai expier ces jours où elle encensait les Baals, où, parée de ses joyaux et de ses atours, elle courait après ses amants et moi, elle m’oubliait! dit l’Eternel.
Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
14 C’Est pourquoi je veux la regagner, en la conduisant dans la solitude, et là je parlerai à son cœur.
“Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
15 Là je lui rendrai ses vignobles, et la Vallée du Malheur deviendra comme la Porte de l’Espérance; elle y entonnera des chants comme aux jours de sa jeunesse, comme au temps où elle sortit du pays d’Egypte.
A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
16 A cette époque, dit l’Eternel, tu m’appelleras: "Mon Epoux"; tu ne m’appelleras plus: "Mon Baal."
“A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
17 Je proscrirai de sa bouche ces dénominations de Baals: leur nom sera voué à l’oubli.
Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
18 A cette époque, je ferai un pacte en leur faveur avec les animaux des champs, avec les oiseaux du ciel et les reptiles de la terre; arcs, épées, tout attirail guerrier, je les briserai dans le pays, et je ferai en sorte que chacun y dormira en paix.
A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
19 Alors, je te fiancerai à moi pour l’éternité; tu seras ma fiancée par la droiture et la justice, par la tendresse et la bienveillance;
Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
20 Ma fiancée en toute loyauté, et alors tu connaîtras l’Eternel.
Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
21 A cette époque, dit l’Eternel, je donnerai, oui, je donnerai satisfaction aux cieux, et ceux-ci combleront les vœux de la terre.
“A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
22 La terre donnera satisfaction au blé, au vin et à l’huile, et ceux-ci combleront les vœux de Jezreël."
ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
23 Et je me complairai à l’implanter dans le pays, je rendrai mon affection à Lo Rouhama, et à Lo Ammi je dirai: "Tu es mon peuple", et lui, il me dira: "Mon Dieu!".
Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”