< Osée 14 >

1 Reviens, Israël, jusqu’à l’Eternel, ton Dieu; car tu n’es tombé que par ton péché.
Ku dawo, ya Isra’ila, ga Ubangiji Allahnku. Zunubanku ne sun zama sanadin fāɗuwarku!
2 Armez-vous de paroles suppliantes et revenez au Seigneur! Dites-lui: "Fais grâce entière à la faute, agrée la réparation nous voulons remplacer les taureaux par cette promesse de nos lèvres.
Ku ɗauki magana tare da ku ku komo wurin Ubangiji. Ku ce masa, “Ka gafarta mana dukan zunubanmu ka kuma karɓe mu da alheri, don mu iya yabe ka da leɓunanmu.
3 Nous ne voulons plus de l’appui d’Achour, nous ne monterons plus sur les chevaux de l’étranger, et nous ne dirons plus: "Nos dieux!" à l’œuvre de nos mains; car auprès de toi seul le délaissé trouve compassion.
Assuriya ba za su iya cece mu ba; ba za mu hau dawakan yaƙi ba. Ba za mu ƙara ce, ‘Allolinmu’ wa abin da hannuwanmu suka yi ba, gama a gare ka ne maraya yakan sami jinƙai.”
4 Alors je les guérirai de leur égarement, je les aimerai avec abandon, parce que ma colère sera désarmée.
“Zan gyara ɓatancinsu in kuma ƙaunace su a sake, gama fushina ya juya daga gare su.
5 Je serai pour Israël comme la rosée, il fleurira comme le lis et enfoncera ses racines comme le cèdre du Liban.
Zan zama kamar raɓa ga Isra’ila zai yi fure kamar lili. Kamar al’ul na Lebanon zai sa saiwarsa zuwa ƙasa;
6 Ses rejetons s’étendront au loin; il aura la beauté de l’olivier, la senteur embaumée du Liban!
tohonsa za su yi girma. Darajarsa za tă zama kamar itacen zaitun, ƙanshinsa kamar al’ul na Lebanon.
7 De nouveau, ceux qu’il abritait à son ombre ranimeront la culture du blé, et s’épanouiront eux-mêmes comme la vigne; il sera renommé comme le vin du Liban.
Mutane za su sāke zauna a inuwarsa. Zai haɓaka kamar ƙwayar hatsi. Zai yi fure kamar kuringa, zai zama sananne kamar ruwan inabi daga Lebanon.
8 Ephraïm, qu’ai-je donc de commun avec les idoles? Moi seul j’exauce, je vois tout; semblable à un cyprès toujours vert, je suis la source de tous tes biens.
Efraim zai ce, me kuma zai haɗa ni da gumaka? Zan amsa masa in kuma lura da shi. Ni kamar koren itacen fir ne; amincinka yana fitowa daga gare ni ne.”
9 Qui est sage pour comprendre ces choses, intelligent pour le reconnaître? Droites sont les voies de l’Eternel, les justes y marchent ferme, les pécheurs y trébuchent."
Wane ne yake da hikima? Zai gane waɗannan abubuwa. Hanyoyin Ubangiji daidai ne; masu adalci sukan yi tafiya a kansu, amma’yan tawaye sukan yi tuntuɓe a kansu.

< Osée 14 >