< Osée 10 >
1 Israël est une vigne dépouillée. On lui avait prodigué les fruits: à mesure que ses fruits augmentaient, il multipliait les autels; plus son pays était prospère, plus ils érigeaient de belles stèles.
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 Leur cœur s’est partagé, ils en portent la peine maintenant; Lui-même abattra leurs autels, ruinera leurs stèles.
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 Ils disent bien à présent: "De roi, nous n’en avons point! Car nous ne craignons pas l’Eternel, et le roi, à quoi peut-il nous servir?"
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 Ils débitent de vains discours, des serments frauduleux, contractent des alliances, et le droit est comme une plante vénéneuse poussant dans les sillons des champs.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 Pour le veau de Beth-Awên, les habitants de Samarie tremblent; oui, ses fidèles sont en deuil à son sujet, ainsi que ses prêtres qui naguère se réjouissaient en lui; car le voilà dépouillé de son éclat.
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 Lui-même, on le transporte en Assyrie, comme présent au roi Protecteur; Ephraïm en recueille la honte, Israël est confus de sa résolution.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 Samarie est réduite à rien de même que son roi, tel un morceau de bois à la surface de l’eau.
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 Les hauts-lieux criminels, le péché visible d’Israël, sont détruits; des ronces et des chardons poussent sur leurs autels. Alors ils diront aux montagnes: "Recouvrez-nous!" et aux collines: "Tombez sur nous!"
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 Plus qu’aux jours de Ghibea, tu as prévariqué, ô Israël! S’Ils s’étaient trouvés là, n’auraient-ils pas été atteints à Ghibea par la guerre dirigée contre les fils de l’iniquité?
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 Au gré de mon désir, je veux les châtier; ils verront des peuples s’attrouper contre eux, pour s’être attachés à leurs deux péchés.
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 Ephraïm est une génisse bien dressée, aimant à fouler le blé; mais moi, je passerai sur son cou superbe, je ferai atteler Ephraïm; il faudra que Juda laboure, que Jacob traîne la herse.
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 Faites vos semailles selon la justice et vous moissonnerez selon la loi d’amour; tracez-vous des sillons. C’Est l’heure de se mettre en quête de l’Eternel, pour qu’il vienne verser sur vous le salut.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 Mais vous avez cultivé l’iniquité et récolté le mal; vous avez mangé le fruit de la tromperie; car tu as eu confiance en ta conduite, dans la multitude de tes guerriers.
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 Aussi le tumulte de la guerre éclatera-t-il contre tes troupes, et toutes tes forteresses seront-elles ruinées, comme Salmân a détruit Beth-Arbêl au jour du combat, où les mères furent écrasées avec leurs enfants.
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 Voilà le sort que vous prépare Béthel, à cause de l’excès de votre perversité. Dès le lever de l’aurore, c’en est complètement fini du roi d’Israël.
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.