< Genèse 7 >

1 L’Éternel dit à Noé: "Entre, toi et toute ta famille, dans l’arche; car c’est toi que j’ai reconnu honnête parmi cette génération."
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
2 De tout quadrupède pur, tu prendras sept couples, le mâle et sa femelle; et des quadrupèdes non purs, deux, le mâle et sa femelle.
Ka ɗauki bakwai na kowace iri tsabtaccen dabba tare da kai, namiji da ta mace, da kuma biyu na kowace dabba marar tsabta, namiji da ta mace,
3 De même, des oiseaux du ciel, respectivement sept, mâles et femelles, pour perpétuer les espèces sur toute la face de la terre.
da kuma bakwai na kowane iri tsuntsu, namiji da ta mace, domin a bar kowane irinsu da rai a dukan duniya.
4 Car encore sept jours, et je ferai pleuvoir sur la terre pendant quarante jours et quarante nuits; et j’effacerai de la surface du sol tous les êtres que j’ai créés.
Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arba’in da dare arba’in, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
5 Noé se conforma à tout ce que lui avait ordonné l’Éternel.
Nuhu ya aikata duk abin da Ubangiji ya umarce shi.
6 Or, il était âgé de six cents ans lorsque arriva le Déluge, ces eaux qui couvrirent la terre.
Nuhu yana da shekaru 106 ne sa’ad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
7 Noé entra avec ses fils, sa femme, et les épouses de ses fils dans l’arche, pour se garantir des eaux du Déluge.
Nuhu da matarsa da’ya’yansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
8 Des quadrupèdes purs; de ceux qui ne le sont point; des oiseaux, et de tout ce qui rampe sur le sol,
Biyu-biyu daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da tsuntsaye da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa,
9 deux à deux ils vinrent vers Noé dans l’arche, mâles et femelles, ainsi que Dieu l’avait prescrit à Noé.
namiji da ta mace, suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi, kamar yadda Allah ya umarce Nuhu.
10 Au bout des sept jours, les eaux du Déluge étaient sur la terre.
Bayan kwana bakwai kuwa ambaliya ruwa ta sauko a bisa duniya.
11 Dans l’année six cent de la vie de Noé, le deuxième mois, le dix-septième jour du mois, en ce jour jaillirent toutes les sources de l’immense Abîme, et les cataractes du ciel s’ouvrirent.
A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe.
12 La pluie tomba sur la terre, quarante jours et quarante nuits.
Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arba’in da dare arba’in.
13 Ce jour-là même étaient entrés dans l’arche: Noé, Sem, Cham et Japhet, fils de Noé, et avec eux la femme de Noé et les trois femmes de ses fils;
A wannan rana Nuhu tare da matarsa da’ya’yansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
14 eux, et toute bête fauve selon son espèce, et tout le bétail selon son espèce, et tout animal rampant sur la terre selon son espèce, et tout volatile selon son espèce: tout oiseau, tout être ailé.
Tare da su kuwa, akwai kowane naman jeji bisa ga irinsa, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinta, da kowane tsuntsun gida da na jeji bisa ga irinsa, da dukan abu mai fiffike.
15 Ils vinrent vers Noé, dans l’arche, deux à deux, de toutes les espèces douées du souffle de vie.
Biyu-biyu na dukan halittu masu numfashi suka zo wurin Nuhu, suka shiga jirgi.
16 Ceux qui entrèrent furent le mâle et la femelle de chaque espèce, comme Dieu l’avait commandé. Alors l’Éternel ferma sur Noé la porte de l’arche.
Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Sa’an nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
17 Le Déluge ayant duré quarante jours sur la terre, les eaux, devenues grosses, soulevèrent l’arche, qui se trouva au-dessus de la terre.
Kwana arba’in ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, sa’ad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
18 Les eaux augmentèrent et grossirent considérablement sur la terre, de sorte que l’arche flotta à la surface des eaux.
Ruwa ya taso, ya ƙaru ƙwarai a duniya, jirgin kuma ya yi ta yawo a bisa ruwa.
19 Puis les eaux redoublèrent d’intensité sur la terre et les plus hautes montagnes qui sont sous le ciel furent submergées.
Ruwa ya ƙaru ƙwarai a duniya, ya kuma rufe dukan duwatsu masu tsawo a ƙarƙashin sammai.
20 De quinze coudées plus haut les eaux s’étaient élevées; et les montagnes avaient disparu.
Ruwan ya taso ya rufe duwatsu, zurfin ruwa daga duwatsun zuwa inda jirgin yake ya fi ƙafa ashirin.
21 Alors périt toute créature se mouvant sur la terre: oiseaux, bétail, bêtes sauvages, tous les êtres pullulant sur la terre, et toute l’espèce humaine.
Kowane abu mai rai da yake tafiya a duniya ya hallaka, tsuntsaye, dabbobin gida, namun jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe a duniya, da kuma dukan mutane.
22 Tout ce qui était animé du souffle de la vie, tout ce qui peuplait le sol, expira.
Kome a busasshiyar ƙasa da yake numfashi a hancinsa ya mutu.
23 Dieu effaça toutes les créatures qui étaient sur la face de la terre, depuis l’homme jusqu’à la brute, jusqu’au reptile, jusqu’à l’oiseau du ciel et ils furent effacés de la terre. Il ne resta que Noé et ce qui était avec lui dans l’arche.
Aka kawar da kowane abu mai rai, mutane da dabbobi da halittu masu rarrafe a ƙasa, da tsuntsayen sama a doron ƙasa, duka aka kawar da su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari da waɗanda suke tare da shi a cikin jirgi.
24 La crue des eaux sur la terre dura cent cinquante jours.
Ruwa ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.

< Genèse 7 >

The Great Flood
The Great Flood