< Ézéchiel 39 >

1 Pour toi, fils de l’homme, prophétise sur Gog et dis: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Me voici contre toi, Gog, prince suzerain de Méchec et de Toubal.
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
2 Je vais t’entraîner, te frapper de vertige et te faire monter de l’extrême Nord et venir sur les montagnes d’Israël.
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
3 Je vais briser ton arc dans ta main gauche et faire tomber tes flèches de ta main droite.
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
4 Sur les montagnes d’Israël tu tomberas, toi et tes légions et les peuples qui t’accompagnent; aux oiseaux de proie de tout plumage, aux fauves des champs je te livre en pâture.
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
5 Sur la surface des champs tu tomberas, oui, c’est moi qui le déclare, dit le Seigneur Dieu.
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 Et j’enverrai un feu dans Magog et parmi ceux qui habitent les plages en toute sécurité, et ils sauront que je suis l’Eternel.
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
7 Et mon saint nom, je le ferai connaître au milieu de mon peuple Israël, et je ne laisserai plus profaner mon saint nom; et les nations reconnaîtront que je suis l’Eternel, saint en Israël!
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
8 La voici venir, elle est accomplie, dit le Seigneur Dieu: C’Est le jour que j’ai annoncé!
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
9 Et ils sortiront, les habitants des villes d’Israël; ils feront du feu et l’attiseront avec les armes de guerre bouclier et rondache, arc et flèches, javelot et lance; ils en alimenteront du feu pendant sept années.
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
10 Ils ne ramasseront pas de bois dans la campagne, ils n’en couperont pas dans les forêts, c’est avec les armures qu’ils feront du feu; et ils dépouilleront leurs spoliateurs et pilleront ceux qui les auront pillés, dit le Seigneur Dieu.
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
11 Et alors, ce jour-là, je donnerai à Gog un lieu de sépulture en Israël la vallée des Passants, à l’Orient de la mer et ce sera une barrière enfermant les passants; on y enterrera Gog et toute sa cohue et on l’appellera "Vallée de la Cohue de Gog".
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
12 La maison d’Israël les ensevelira, pour purifier le pays, pendant sept mois.
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
13 Tous les gens du pays aideront à l’inhumation et s’en feront honneur, au jour de ma glorification, dit le Seigneur Dieu.
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
14 Puis on désignera des hommes en permanence, ayant mission de parcourir le pays pour enterrer ces passants, ceux qui seraient restés sur la surface du sol, afin de le purifier. C’Est au bout de sept mois qu’ils commenceront la recherche.
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
15 En parcourant ainsi le pays, quand l’un d’eux apercevra des ossements humains, il bâtira à côté un cippe, jusqu’à ce que les fossoyeurs les aient ensevelis dans la Vallée de la Cohue.
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
16 Pareillement, la ville sera nommée "Hamôna!", et l’on purifiera le pays.
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
17 Et toi, fils de l’homme, ainsi parle le Seigneur Dieu: Dis aux oiseaux de tout plumage et à toutes les bêtes des champs: Rassemblez-vous et venez! Réunissez-vous de toutes parts auprès de mon hécatombe que je prépare pour vous. Une grande hécatombe sur les montagnes d’Israël, vous mangerez de la chair et vous boirez du sang.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
18 Vous mangerez la chair des guerriers, vous boirez le sang des princes de la terre, tous béliers, agneaux gras, boucs, taureaux, bétail plantureux de Basan.
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
19 Vous mangerez de la graisse à satiété et vous boirez du sang jusqu’à l’ivresse, grâce à l’hécatombe que j’aurai préparée pour vous.
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
20 Vous vous gorgerez à ma table de chevaux et d’attelages, de soldats et de toute espèce de gens de guerre, dit le Seigneur Dieu.
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 Et je manifesterai ma gloire parmi les nations, et tous les peuples verront le jugement que j’ai exercé et la main que j’ai posée sur eux.
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
22 Et la maison d’Israël saura que je suis l’Eternel, leur Dieu, à dater de ce jour et ultérieurement.
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
23 Et les nations sauront que c’est à cause de son iniquité que la maison d’Israël avait été exilée, parce qu’ils m’ont été infidèles, de sorte que je détournai d’eux ma face et les livrai au pouvoir de leurs ennemis, et qu’ils tombèrent tous sous le glaive.
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
24 Selon leurs souillures et leurs péchés, je les ai traités, et j’ai détourné d’eux ma face.
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
25 En vérité, ainsi parle le Seigneur Dieu, maintenant je ferai revenir Jacob de captivité, je prendrai en pitié toute la maison d’Israël et j’aurai le souci jaloux de mon nom.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
26 Ils auront expié leur opprobre et toute l’infidélité dont ils se sont rendus coupables à mon égard, une fois qu’ils habiteront de nouveau sur leur sol en toute sécurité, sans personne pour les troubler.
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
27 Quand je les ramènerai d’entre les peuples et que je les ferai sortir ensemble des pays de leurs ennemis, je serai sanctifié par eux aux yeux de nations nombreuses.
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
28 Ils sauront que je suis l’Eternel, leur Dieu, quand, après les avoir exilés parmi les nations, je les aurai réintégrés dans leur pays, sans plus laisser personne d’entre eux là-bas.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
29 Et je ne détournerai plus d’eux ma face, par la raison que j’aurai répandu mon esprit sur la maison d’Israël, dit le Seigneur Dieu."
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 39 >