< Ézéchiel 35 >

1 La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Fils de l’homme, dirige ta face vers la montagne de Séir et prophétise sur elle.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
3 Tu lui diras: Ainsi parle le Seigneur Dieu Me voici contre toi, montagne de Séir! J’Étendrai ma main sur toi et je ferai de toi une solitude et un désert.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
4 De tes villes je ferai une ruine, et toi, tu seras une solitude; tu sauras ainsi que je suis l’Eternel.
Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
5 Parce que tu nourrissais une haine invétérée et que tu as précipité les enfants d’Israël sous le tranchant de l’épée, au jour de leur malheur, à l’heure où le crime a pris fin,
“‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
6 c’est pourquoi, par ma vie, dit le Seigneur Dieu, je te mettrai à sang et le sang te poursuivra! Puisque tu n’as pas eu horreur du sang, le sang te poursuivra!
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
7 Je ferai de la montagne de Séir un désert et une solitude, et j’en extirperai tout allant et venant.
Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
8 Je joncherai ses hauteurs de ses cadavres; sur tes collines et tes vallées, dans tous tes ravins tomberont les victimes du glaive.
Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
9 Je ferai de toi des ruines éternelles et tes villes ne seront pas restaurées; ainsi vous saurez que je suis l’Eternel.
Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
10 Parce que tu disais: "Les deux nations et les deux pays seront à moi et nous en hériterons", —or, l’Eternel était là
“‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
11 c’est pourquoi, par ma vie, dit le Seigneur Dieu, j’agirai conformément à ta fureur et à ta jalousie qui t’ont fait agir dans la haine que tu leur portais, et je me ferai connaître parmi eux, lorsque je te jugerai.
saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
12 Et tu sauras que moi, l’Eternel, j’ai entendu tous tes outrages, que tu as proférés contre les montagnes d’Israël, en disant: "Elles sont dévastées, c’est à nous qu’elles sont livrées en proie!"
Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
13 Vous en avez eu plein la bouche contre moi, vous avez accumulé contre moi vos propos; moi, je l’ai bien entendu."
Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
14 Ainsi donc parle le Seigneur Dieu: "Pendant que toute la terre sera dans la joie, je ferai de toi un désert.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
15 De même que tu t’es réjoui au sujet de l’héritage de la maison d’Israël, parce qu’il était dévasté, ainsi te ferai-je: tu seras une solitude, montagne de Séir, ainsi qu’Edom tout entier. Ils sauront alors que je suis l’Eternel."
Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”

< Ézéchiel 35 >