< Ézéchiel 32 >

1 Il advint, dans la douzième année, le premier jour du douzième mois, que la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Fils de l’homme, entonne une complainte sur Pharaon, roi d’Egypte, et dis-lui: Lion des nations, tu es perdu! Et pourtant tu étais comme le crocodile dans les mers, tu t’élançais avec tes fleuves, tu troublais les eaux de tes pieds et tu en agitais les flots."
“Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
3 Ainsi parle le Seigneur Dieu: "J’Étendrai sur toi mon filet avec le concours de peuples nombreux qui te haleront dans ma nasse.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
4 Et je te laisserai là sur le sol, je te lancerai sur la surface des champs, je ferai s’abattre sur toi tous les oiseaux du ciel et je rassasierai de toi toutes les bêtes de la terre.
Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
5 J’Exposerai ta chair sur les montagnes, et je remplirai les vallées de ton cadavre.
Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
6 Le pays de tes ébats, je l’arroserai de ton sang jusqu’aux montagnes, et les ravins seront pleins de toi.
Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
7 Par suite de ton extinction, je voilerai les cieux et j’assombrirai leurs étoiles; le soleil, je le couvrirai de nuées et la lune ne fera plus briller son éclat.
Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
8 Tous les flambeaux lumineux au ciel, je les obscurcirai à cause de toi et je répandrai les ténèbres sur ton pays, dit le Seigneur Dieu.
Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Je contristerai le coeur de peuples nombreux, quand je ferai parvenir l’annonce de ta ruine parmi les nations, dans des pays que tu ne connais point.
Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
10 A cause de toi, je frapperai de stupeur quantité de peuples: à cause de toi, leurs rois seront saisis d’horreur, quand je ferai voltiger mon glaive devant leur face. Ils trembleront à tout instant, chacun pour sa personne, au jour de ta chute."
Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
11 Car ainsi parle le Seigneur Dieu: "Le glaive du roi de Babylone fondra sur toi.
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
12 Sous les glaives des vaillants guerriers, tous gens terribles entre les nations, je ferai tomber ta multitude; ils ruineront l’orgueil de l’Egypte, et toute sa multitude périra.
Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
13 J’Anéantirai tout son bétail auprès des grandes eaux, et celles-ci ne seront plus troublées par le pied de l’homme, elles ne seront plus troublées par les sabots des animaux.
Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
14 Alors, je ferai rasseoir leurs flots, et les fleuves, je les ferai couler comme l’huile, dit le Seigneur Dieu.
Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Quand je réduirai la terre d’Egypte en ruines, et que le pays sera dépouillé de ce qu’il contient, quand je frapperai tous ceux qui l’habitent, on saura que c’est moi l’Eternel.
Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
16 C’Est là la complainte que l’on chantera, que chanteront les filles des nations. Elles la chanteront sur l’Egypte et sur toute sa multitude, dit le Seigneur Dieu."
“Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
17 Il advint, dans la douzième année, le quinze du mois, que la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 "Fils de l’homme, consacre une lamentation à la multitude de l’Egypte et précipite-la, elle et les filles de nations puissantes, dans les régions souterraines avec ceux qui descendent dans la fosse.
“Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
19 Qui dépasses-tu en agrément? Descends! Couche-toi avec des incirconcis!
Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
20 Ils tombent parmi les victimes du glaive; au glaive elle est livrée; entraînez-la avec toutes ses multitudes!
Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
21 Les puissants guerriers, du fond du Scheol, l’interpellent avec ses alliés: "Ils sont descendus disent-ils, ils se sont couchés les incirconcis, victimes du glaive!" (Sheol h7585)
Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol h7585)
22 Là est Achour avec toute sa troupe: autour de lui sont ses tombeaux; ce sont tous des victimes tombées sous le glaive,
“Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
23 dont les sépulcres ont été placés au fond de la fosse, et la troupe rangée autour de son tombeau; ce sont tous des victimes tombées sous le glaive, eux qui avaient porté la terreur au pays des vivants.
Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
24 Là est Elam avec toute sa multitude à l’entour de son sépulcre; ce sont tous des victimes tombées sous le glaive; ils sont descendus incirconcis dans les profondeurs souterraines, eux qui avaient porté la terreur au pays des vivants; ils subissent leur opprobre avec ceux qui sont descendus dans la fosse.
“Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
25 Au milieu des cadavres, on lui a donné une couche, avec toute sa multitude dans des tombes tout autour; ce sont tous des incirconcis, victimes du glaive, car leur terreur s’est répandue dans le pays des vivants; ils subissent leur opprobre avec ceux qui sont descendus dans la fosse; au milieu des cadavres, elle a été placée.
An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
26 Là est Méchec, là est Toubal et toute sa multitude; autour de lui ses tombeaux. Ce sont tous des incirconcis, victimes du glaive, car ils ont porté leur terreur au pays des vivants.
“Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
27 Mais ils ne reposent pas avec les héros qui sont tombés parmi les incirconcis, qui sont descendus au tombeau avec leur attirail de guerre, à qui on a mis leurs glaives sous la tête; leurs crimes sont restés sur leurs ossements, car la terreur des héros a été au pays des vivants. (Sheol h7585)
Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol h7585)
28 Et toi, au milieu des incirconcis tu seras brisé, et tu te coucheras avec les victimes du glaive.
“Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
29 Là est Edom, avec ses rois et tous ses princes qui ont été mis, en dépit de leur force, avec les victimes du glaive; ceux-là reposent avec les incirconcis et ceux qui sont descendus dans la fosse.
“Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
30 Là sont les princes du Nord au complet et tous les Sidoniens qui sont descendus avec les corps morts, confondus malgré la terreur que leur vigueur inspirait; ils se sont couchés, incirconcis, avec les victimes du glaive, et ils ont porté leur opprobre avec ceux qui sont descendus dans la fosse.
“Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
31 Pharaon les verra et se consolera au sujet de toute sa multitude; ils seront victimes du glaive, Pharaon et toute son armée, dit le Seigneur Dieu.
“Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
32 Car j’ai répandu ma terreur au pays des vivants; et il sera couché parmi les incirconcis, avec les victimes du glaive, Pharaon et toute sa multitude, dit le Seigneur Dieu."
Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 32 >