< Ézéchiel 30 >
1 La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Fils de l’homme, prophétise et dis: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Lamentez-vous! Hélas, quel jour!
“Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
3 Car un jour est proche, oui, un jour est proche, fixé par l’Eternel, un jour de nuée: ce sera l’heure des nations.
Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
4 Le glaive s’abattra sur l’Egypte; il y aura de l’épouvante en Ethiopie, quand tomberont les victimes en Egypte. On prendra ses richesses, ses fondements seront renversés.
Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
5 L’Ethiopie, Pout et Loud, tout l’Occident, et Koub avec les fils du pays de l’Alliance tomberont sous le glaive.
Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
6 Ainsi parle l’Eternel: "Les appuis de l’Egypte s’écrouleront, et sa fière puissance sera abaissée. De Migdol à Syène, ils y tomberont sous le glaive, dit le Seigneur Dieu.
“‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
7 Ils seront dévastés entre les pays dévastés, et ses villes seront au nombre des villes ruinées.
Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
8 Et ils sauront que je suis l’Eternel, lorsque je mettrai le feu à l’Egypte et que tous ses auxiliaires seront brisés.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
9 Ce jour-là, des messagers partiront au-devant de moi dans des navires, pour troubler l’Ethiopie dans sa quiétude, et il y aura une terreur parmi eux au jour de l’Egypte, car le voici venir!"
“‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
10 Ainsi parle le Seigneur Dieu: "J’Abolirai la richesse de l’Egypte par la main de Nabuchodonosor, roi de Babylone.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
11 Lui et son peuple avec lui, les plus violents des peuples, seront amenés pour détruire le pays; ils tireront leurs glaives contre l’Egypte et rempliront le pays de cadavres.
Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
12 Je mettrai les cours d’eau à sec et je livrerai le pays à la merci de barbares; je dévasterai le pays avec ce qu’il renferme par la main d’étrangers, c’est moi, l’Eternel, qui le dis."
Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
13 Ainsi parle le Seigneur Dieu: "J’Anéantirai les idoles, je ferai disparaître les faux dieux de Nof et le prince du pays d’Egypte: il n’y en aura plus. Je répandrai la terreur dans le pays d’Egypte.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
14 Je ruinerai Pathros, je mettrai le feu à Çoân et j’infligerai des châtiments à Nô.
Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
15 Je déverserai ma colère sur Sîn, forteresse de l’Egypte, et j’extirperai le peuple de Nô.
Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
16 Je mettrai le feu à l’Egypte, Sin sera saisie de tremblement, Nô est pour être prise d’assaut, Nof sera livrée aux ennemis en plein jour.
Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
17 Les jeunes gens d’Avên et de Pibécet tomberont sous le glaive, et elles-mêmes Won; en captivité.
Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
18 Et dans Tehafnehès, le jour sera ténébreux, quand j’y briserai les appuis de l’Egypte et que sera aboli en elle l’orgueil de sa puissance, une nuée la couvrira et ses filles iront en captivité.
Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
19 Et j’exercerai des sévices sur l’Egypte, et ils sauront que c’est moi l’Eternel."
Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
20 II advint, la onzième année, le sept du premier mois, que la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
21 "Fils de l’homme, j’ai brisé le bras de Pharaon, roi d’Egypte; or, on ne l’a point pansé en y appliquant des médicaments, en y posant un bandage comme pansement, afin qu’il reprenne des forces pour tenir une épée.
“Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
22 C’Est pourquoi, ainsi parle l’Eternel Dieu, je m’en prends à Pharaon, roi d’Egypte; je briserai ses bras, et celui qui est valide et celui qui est fracturé, et je lui ferai tomber l’épée de la main.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
23 Je disperserai les Egyptiens parmi les peuples, je les disséminerai dans les pays.
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
24 Mais j’affermirai les bras du roi de Babylone et je mettrai mon épée dans sa main, tandis que je briserai les bras de Pharaon, de telle sorte qu’il râlera devant lui du râle de l’homme frappé à mort.
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
25 Oui, je fortifierai les bras du roi de Babylone alors que les bras de Pharaon tomberont, et on saura que c’est moi l’Eternel, quand je mettrai mon glaive dans la main du roi de Babylone, et qu’il le brandira contre le pays d’Egypte.
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
26 Et je disperserai les Egyptiens parmi les nations, je les disséminerai dans les pays, et ils sauront que je suis l’Eternel."
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”