< Ézéchiel 3 >

1 Et il me dit: "Fils de l’homme, mange ce que tu trouves là, mange ce rouleau et va parler à la maison d’Israël."
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
2 J’Ouvris la bouche, et il me fit manger ce rouleau.
Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
3 Et il me dit: "Fils de l’homme, tu nourriras ton ventre' et rempliras tes entrailles de ce rouleau que je te donne"; je le mangeai et il devint dans ma bouche aussi doux que du miel.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
4 Il me dit encore: "Fils de l’homme, debout! Va auprès de la maison d’Israël et communique-leur mes paroles.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
5 Car ce n’est pas comme à un peuple à l’idiome obscur et à la langue lourde que tu es envoyé à la maison d’Israël.
Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
6 Ce n’est pas à des peuples nombreux au langage obscur et à la langue lourde, dont tu ne comprends pas les paroles; si à ceux-là je t’envoyais, eux, ils t’écouteraient.
ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
7 Mais la maison d’Israël ne consentira pas à t’écouter, car ils ne veulent pas m’écouter; car la maison d’Israël tout entière a le front rétif et le coeur endurci.
Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
8 Voici que je rendrai ton visage résolu en face de leurs visages et ton front résolu en face de leur front.
Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
9 Comme le diamant plus dur que le roc, je ferai ton front. Tu n’auras pas peur d’eux, tu ne trembleras pas à cause d’eux, parce qu’ils sont une maison de rébellion.
Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
10 Et il me dit: "Fils de l’homme, toutes les paroles que je te dirai, accueille-les dans ton coeur et écoute-les de tes oreilles.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
11 Et va-t-en trouver les exilés, les fils de ton peuple, et tu: leur diras: "Ainsi a parlé le Seigneur Dieu," soit qu’ils écoutent, soit qu’ils refusent."
Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
12 Et l’esprit m’emporta et j’entendis derrière moi le bruit d’un grand tumulte: "Bénie soit la gloire de l’Eternel en son lieu!"
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
13 Et le bruit des ailes des Haïot qui se joignaient l’une l’autre et le bruit des roues vis-à-vis d’elles et le bruit d’un grand tumulte.
Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
14 Et l’esprit m’éleva en l’air et m’emporta, et je m’en allai, triste, dans l’exaltation de mon esprit, et la main du Seigneur pesait sur moi fortement.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
15 Et j’allai vers les exilés à Tel-Abib, vers ceux qui demeurent près du fleuve de Kebar, et là où ils étaient assis, je demeurai pendant sept jours, affligé, au milieu d’eux.
Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
16 Il advint au bout de sept jours que la parole du Seigneur me fut adressée en ces termes:
A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
17 "Fils de l’homme, je t’ai placé en sentinelle sur la maison d’Israël, tu écouteras ce que ma bouche dira, et tu les admonesteras de ma part.
“Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
18 Quand je dirai à l’impie: "Oui, tu mourras!" si tu ne l’as pas averti, si tu n’as pas parlé afin de détourner par tes exhortations le méchant de sa mauvaise voie et de sauver sa vie, le méchant mourra dans son iniquité, mais de son sang, je te demanderai compte.
In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
19 Mais si toi, tu avertis le méchant et qu’il ne revienne pas de son iniquité et de sa voie mauvaise, lui mourra dans son péché, et toi, tu auras la vie sauve.
Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
20 Et quand le juste se sera détourné de sa vertu pour faire le mal, je mettrai un obstacle devant lui et il mourra parce que tu ne l’auras pas averti, il mourra dans son péché et les actes de vertu qu’il a accomplis ne seront pas mentionnés, mais de son sang, je te demanderai compte.
“Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
21 Mais que si toi tu avertis le juste pour que le juste ne pèche pas, et qu’en effet, il ne pèche pas, certes, il vivra, pour avoir été mis en garde, et toi, tu auras la vie sauve."
Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
22 Et la main du Seigneur fut sur moi en ce lieu et il me dit: "Lève-toi, sors vers la plaine et là je te parlerai"
Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
23 Et je me levai et je sortis vers la plaine, et voici que là se tenait la gloire de l’Eternel, comme la gloire que j’avais vue sur le fleuve de Kebar, et je tombai sur ma face.
Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
24 Et l’esprit vint en moi et me fit dresser sur mes pieds, et Dieu me parla et me dit: "Viens, enferme-toi dans ta maison.
Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
25 Et toi, fils de l’homme, voici qu’ils mettront sur toi des cordes avec lesquelles ils te lieront et tu ne sortiras pas parmi eux.
Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
26 Et j’attacherai ta langue à ton palais, tu deviendras muet, et tu ne leur seras pas un sermonneur, car ils sont une maison de rébellion.
Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
27 Mais quand je te parlerai, j’ouvrirai ta bouche et tu leur diras: "Ainsi parle le Seigneur Dieu: Ecoute qui veut écouter, refuse d’entendre qui veut refuser! Car ils sont une maison de rébellion!"
Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.

< Ézéchiel 3 >