< Ézéchiel 29 >
1 Dans la dixième année, le dixième mois, le douze du mois, la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Fils de l’homme, dirige ta face contre Pharaon, roi d’Egypte, et prophétise sur lui et sur l’Egypte entière.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Prononce ces paroles: Ainsi parle le Seigneur Dieu: Voici, je m’en prends à toi, Pharaon, roi d’Egypte, grand crocodile, couché au milieu de tes fleuves, toi qui dis: "Mon fleuve est à moi, c’est moi qui me le suis fait!"
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 Je passerai des crochets à tes mâchoires, je collerai à tes écailles les poissons de tes fleuves. Je te tirerai du milieu de tes fleuves, et tous les poissons de tes fleuves adhéreront à tes écailles.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 Et je te jetterai dans le désert, toi et tous les poissons de tes fleuves; tu tomberas sur la surface des champs, tu ne seras ni ramassé ni recueilli. Aux bêtes de la terre et aux oiseaux du ciel, je t’ai donné en pâture.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 Tous les habitants d’Egypte sauront alors que c’est moi l’Eternel, parce qu’ils avaient prêté un appui de roseau à la maison d’Israël.
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 Lorsqu’ils te saisissent par la main, tu te romps et tu leur transperces toutes les épaules; lorsqu’ils s’appuient sur toi, tu te brises, et tu leur paralyses tous les reins.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 C’Est pourquoi, ainsi parle le Seigneur Dieu, voici, je vais susciter contre toi l’épée et retrancher de toi hommes et bêtes:
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 Le pays d’Egypte deviendra une solitude et une ruine, et l’on saura que c’est moi l’Eternel parce qu’il a dit: "Le fleuve est à moi, et c’est moi qui l’ai fait."
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 Oui, certes, je m’en prends à toi et à tes fleuves et je ferai du pays d’Egypte des ruines désolées et solitaires, de Migdol à Syène et aux confins de l’Ethiopie.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 Nul pied d’homme ne la foulera, nul animal n’y portera ses pas: il ne sera plus habité pendant quarante années.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 Je rendrai le pays d’Egypte désolé entre les pays désolés, et ses villes, parmi les villes ruinées, seront une solitude durant quarante années; je disperserai les Egyptiens parmi les peuples, je les disséminerai dans les pays.
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 Oui, ainsi parle le Seigneur Dieu, au bout de quarante années, je rassemblerai les Egyptiens du milieu des nations où ils auront été dispersés.
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 Je ramènerai les captifs égyptiens et je les rétablirai sur la terre de Pathros, leur pays d’origine; mais ils n’y formeront qu’un humble royaume.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 Plus que les autres royaumes, il sera humble, et il ne s’élèvera plus au-dessus des peuples. Je veux les diminuer pour qu’ils ne dominent plus les peuples.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 Et il ne sera plus pour la maison d’Israël un sujet' de confiance, ravivant le souvenir de la faute commise quand ils se tournaient vers eux, et on saura alors que c’est moi le Seigneur Dieu."
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 II advint, dans la vingt-septième année, le premier du premier mois, que la parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 "Fils de l’homme, Nabuchodonosor, roi de Babylone, a fait faire à son armée une rude besogne contre Tyr; toutes les têtes en sont devenues chauves, toutes les épaules sont meurtries. Or, lut ni son armée n’ont recueilli de salaire de Tyr pour la besogne qu’il a faite contre elle.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Donc, ainsi parle le Seigneur Dieu, voici, je vais livrer à Nabuchodonosor, roi de Babylone, le pays d’Egypte, pour qu’il puisse en emporter les richesses, en prendre le butin et le mettre au pillage: ce sera le salaire de son armée.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 Comme prix de son labeur, qu’il a accompli contre Tyr, je lui donne le pays d’Egypte, parce qu’ils ont travaillé pour moi, dit le Seigneur Dieu.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 Ce jour-là, je relèverai la puissance de la maison d’Israël. Quant à toi, je justifierai pleinement tes paroles au milieu d’eux, et ils sauront que c’est moi l’Eternel."
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”