< Ézéchiel 23 >

1 La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Fils de l’homme, il y avait deux femmes, filles d’une même mère.
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 Elles se prostituèrent en Egypte, dans leur jeunesse elles s’y prostituèrent; là furent pressées leurs mamelles, là on étreignit leur sein virginal.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 Elles s’appelaient, l’aînée, Ohola, et sa sœur, Oholiba; elles m’appartinrent et enfantèrent des fils et des filles: leurs noms, c’étaient Samarie pour Ohola et Jérusalem pour Oholiba.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 Ohola se débaucha, alors qu’elle était en ma puissance; elle s’engoua de ceux qui la courtisaient, des Assyriens qui l’approchaient,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 gens habillés d’azur, gouverneurs et seigneurs, tous jouvenceaux séduisants, cavaliers montant des chevaux.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 Elle leur prodigua ses faveurs impures, à tous ces fils distingués d’Achour, et à cause de tous ceux dont elle était éprise elle se souilla par leurs idoles.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Pourtant elle ne renonça point à ses dérèglements datant de l’Egypte; car ils avaient eu commerce avec elle dans sa jeunesse, ils avaient étreint son sein virginal et répandu leur impudicité sur elle.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 C’Est pourquoi je l’ai livrée entre les mains de ses amants, entre les mains des fils d’Achour, dont elle s’était éprise.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 Ceux-ci découvrirent sa nudité, prirent ses fils et ses filles, et elle-même, ils la firent périr par l’épée. Elle devint un exemple mémorable pour les femmes, et on lui infligea de justes châtiments.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 Or, sa soeur Oholiba en avait été témoin; et elle s’adonna à des amours encore plus coupables, à un dévergondage pire que celui de sa soeur.
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 Elle s’éprit des fils d’Achour, des gouverneurs et seigneurs qui l’approchaient, vêtus magnifiquement, cavaliers montant des chevaux, tous jouvenceaux séduisants.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 Je constatai qu’elle s’était souillée: même conduite chez toutes deux.
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 Elle enchérit sur son inconduite, quand elle vit des hommes dessinés sur la muraille, des images de Chaldéens peintes en vermillon,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 portant des ceintures attachées aux reins, des turbans étalés sur leur tête, ayant tous l’apparence de capitaines, fidèle peinture des fils de Babel, dont la Chaldée est le pays natal.
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 Elle se prit d’amour pour eux, fascinée par ce qu’elle voyait, et elle leur dépêcha des messagers en Chaldée.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 Les fils de Babel vinrent à elle pour un commerce d’amour, et la souillèrent par leur luxure; elle reçut d’eux une souillure, puis son âme se détacha d’eux.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Elle étala ses débauches, elle découvrit sa honte, et mon âme se détacha d’elle comme mon âme s’était détachée de sa soeur.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 Elle redoubla ses dérèglements, en souvenir des jours de sa jeunesse, où elle s’était prostituée dans le pays d’Egypte.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 Elle s’engoua de leurs compagnons de débauche, qui ont une chair comme celle des ânes et dont la lubricité égale celle des chevaux.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 Et ainsi tu ravivas la mémoire de la débauche de ta jeunesse, quand les Egyptiens pressaient tes mamelles, à cause de ton sein virginal.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 C’Est pourquoi, Oholiba, ainsi parle le Seigneur Dieu: Voici que je vais exciter contre toi tes amants, ceux dont s’était détaché ton coeur, et les amener de toutes parts contre toi:
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 les fils de Babel et tous les Chaldéens, Pekod et Choa et Koa, et tous les fils d’Achour avec eux, ces jeunes hommes séduisants, tous gouverneurs et seigneurs, officiers et dignitaires, tous montant des chevaux.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 Ils viendront contre toi avec armes, chars et roues, avec une multitude de peuples; ils t’envelopperont d’un cercle de boucliers, d’écus et de casques. Je leur exposerai la cause, et ils te jugeront selon leurs coutumes.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 Je dirigerai mon zèle jaloux contre toi, et ils te traiteront avec fureur, ils t’arracheront le nez et les oreilles, et ce qui restera de toi tombera par l’épée; ils te prendront tes fils et tes filles, et ton reste sera consumé par le feu.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 Ils te dépouilleront de tes 'vêtements et s’empareront de tes objets de parure.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 Ainsi Je mettrai fin à ton infamie et à tes débauches originaires du pays d’Egypte; tu ne lèveras plus les yeux vers eux, et de l’Egypte tu ne te souviendras plus."
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 C’Est que le Seigneur Dieu parle de la sorte: "Je vais te livrer dans la main de ceux que tu détestes, dans la main de ceux dont s’est détachée ton âme.
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 Ils te traiteront avec haine, prendront tout le fruit de ton labeur et te laisseront là, nue et dépouillée; la honte de tes luxures sera découverte, ton infamie et tes dérèglements.
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 On en agira ainsi avec toi, parce que tu t’es prostituée aux nations, parce que tu t’es souillée par leurs idoles.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Tu as suivi la voie de ta soeur; je mettrai donc sa coupe dans ta main."
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 Ainsi parle le Seigneur Dieu: "Tu boiras la coupe de ta soeur, si profonde et si large; elle sera une cause de risée et de moquerie, cette coupe au grand contenu.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Tu seras remplie d’ivresse et de peine; c’est une coupe de ruine et de désolation, la coupe de ta soeur Samarie.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 Tu la boiras jusqu’à la dernière goutte, tu en rongeras les tessons et tu te déchireras les seins, car c’est moi qui parle", dit le Seigneur Dieu.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 Oui certes, ainsi parle le Seigneur Dieu: "Puisque tu m’as oublié et que tu m’as rejeté derrière ton dos, porte donc, toi aussi, la peine de ton infamie et de tes dérèglements."
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 L’Eternel me dit: "Fils de l’homme, veux-tu faire le procès de Ohola et de Oholiba? Expose-leur leurs abominations.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 Elles ont forniqué, il y a du sang sur leurs mains; elles ont forniqué avec leurs idoles et sont allées jusqu’à leur livrer en pâture leurs fils, qu’elles m’avaient enfantés.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 Elles m’ont fait ceci encore: elles ont souillé mon sanctuaire ce même jour et profané mes sabbats.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 Oui, lorsqu’elles immolaient leurs fils à leurs idoles, elles entraient le même jour dans mon sanctuaire pour le profaner; voilà comme elles en ont agi dans ma maison.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 Bien plus, elles envoyaient chercher des hommes qui venaient de loin; un ambassadeur leur était dépêché, et ils arrivaient ceux pour qui tu t’étais baignée, tu t’étais enduit les yeux de fard, et tu avais revêtu tes atours.
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 Et tu prenais place sur un lit d’apparat, devant lequel une table était dressée, où tu posais mon encens et mon huile.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 On entendait chez elle le bruit d’une multitude paisible, et aux gens d’une nombreuse foule venaient encore s’ajouter des buveurs amenés du désert; alors elles mettaient des bracelets à leurs bras et une couronne magnifique sur leur tête.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 Et j’ai dit de celle qui est flétrie par son inconduite: Encore maintenant on se livre avec elle aux débauches habituelles.
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 On venait vers elle comme on vient vers une femme prostituée; ainsi on est venu vers Ohola et Oholiba, femmes de mauvaises moeurs.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 Or ce seront des hommes justes qui leur appliqueront la peine des adultères et 'la peine de celles qui versent le sang; car elles sont adultères et il y a du sang sur leurs mains."
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 En effet, ainsi parle le Seigneur Dieu: "Qu’on fasse monter contre elles une grande foule et qu’on les livre à la terreur et au pillage!
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 Que cette Moule les accable sous les pierres et les transperce par les glaives, qu’on fasse périr leurs fils et leurs filles et mettre le feu à leurs maisons!
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 Ainsi je purgerai le pays de la débauche, toutes les femmes recevront une leçon et elles n’imiteront point votre inconduite.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 On vous chargera du poids de votre débauche, vous porterez la peine de vos odieuses idoles, et vous reconnaîtrez que je suis le Seigneur Dieu."
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Ézéchiel 23 >