< Ézéchiel 21 >

1 La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 "Fils de l’homme, dirige ta face vers Jérusalem, prêche sur les sanctuaires et prophétise sur la terre d’Israël.
“Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
3 Tu diras au pays d’Israël: Ainsi parle l’Eternel: Me voici contre toi, je sortirai mon épée de son fourreau et j’extirperai de toi justes et impies.
ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
4 Parce que je veux extirper de toi justes et impies, c’est pourquoi mon épée sortira de son fourreau contre toute chair du Sud au Nord.
Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
5 Et toute chair saura que c’est moi, l’Eternel, qui ai tiré mon épée du fourreau: elle n’y rentrera plus.
Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
6 Et toi, fils de l’homme, pousse des soupirs: les reins brisés, dans l’amertume, pousse des soupirs à leurs yeux.
“Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
7 Alors s’ils te disent: "Pourquoi soupires-tu?" tu répondras: "C’Est à cause de la nouvelle qui arrive, qui fait fondre tous les coeurs, défaillir toutes les mains, se troubler tous les esprits, s’en aller en eau tous les genoux; elle arrive et s’accomplit dit le Seigneur Dieu."
Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
8 La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 "Fils de l’homme, prophétise et dis: Ainsi parle le Seigneur: Dis qu’une épée, une épée a été aiguisée et polie.
“Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
10 C’Est pour procéder à la tuerie qu’elle a été aiguisée, c’est pour qu’elle jette des éclairs qu’elle a été polie. Ou se peut-il que nous connaissions encore la joie? La verge qui frappe mon fils voit avec dédain tout instrument de bois.
wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
11 Il l’a donnée à polir pour qu’on la saisisse par la main; on l’a aiguisée, l’épée, et on l’a polie pour la mettre en la main du meurtrier.
“‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
12 Crie et lamente-toi, fils de l’homme, car cette épée a sévi sur mon peuple, elle a sévi sur tous les princes d’Israël; ils ont été livrés à l’épée avec mon peuple, c’est pourquoi frappe-toi la hanche.
Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
13 C’Est une épreuve. Et que sera-ce s’il s’y ajoute la verge dédaigneuse? Rien ne sera plus, dit le Seigneur Dieu.
“‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
14 Et toi, fils de l’homme, prophétise et frappe d’une main contre l’autre et que l’épée redouble ses coups par trois fois! C’Est une épée de massacres, l’épée de la grande victime qui les pourchasse.
“Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
15 C’Est afin de faire fondre les coeurs et de multiplier les chutes auprès de toutes leurs portes, que j’ai brandi le brillant de l’épée; ah! Elle est préparée pour étinceler et aiguisée pour tuer.
Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
16 Sois tranchante à droite, avance à gauche, partout où tes lames sont dirigées.
Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
17 Et moi aussi, je frapperai d’une main contre l’autre et j’assouvirai ma colère, moi, l’Eternel, je l’ai dit."
Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
18 La parole de l’Eternel me fut adressée en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
19 "O toi, fils de l’homme, fais-toi deux chemins par où vienne l’épée du roi de Babylone; ils doivent partir tous deux d’un même pays; et grave une main indicatrice, grave-la au point de départ du chemin de la ville.
“Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
20 Fais un chemin par où vienne l’épée contre Rabba capitale des fils d’Ammon et contre Juda dans Jérusalem la forte.
Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
21 Car le roi de Babylone s’est porté à la naissance du chemin, au commencement des deux chemins, pour consulter le sort; il a agité les flèches, interrogé les Teraphim, examiné le foie.
Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
22 Dans sa main droite se trouvait le sort "Jérusalem" pour y dresser des béliers, y proclamer la tuerie, pour y proférer des cris de guerre, pour dresser des béliers contre (es portes, pour y jeter une chaussée et bâtir des ouvrages de siège.
A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
23 Mais cela paraîtra à leurs yeux un sort mensonger, on leur a fait serments sur serments; mais lui leur rappellera leur crime, pour qu’ils soient capturés.
Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
24 C’Est pourquoi, ainsi parle le Seigneur Dieu, puisque vous avez réveillé le souvenir de votre crime, en dévoilant vos fautes, en montrant à nu vos péchés dans toutes vos actions, puisqu’il est fait mention de vous, vous serez capturés par la main.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
25 Et toi, impie, désigné à la mort, prince d’Israël dont le jour est venu, à l’heure où ton crime prend fin,
“‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
26 ainsi parle le Seigneur Dieu: Bas la tiare, plus de couronne! Tout à l’inverse! Que ce qui est bas s’élève, que ce qui est élevé s’abaisse!
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
27 Ruine, ruine, ruine, voilà ce que j’en ferai; cela non plus n’existe plus, jusqu’à ce que vienne celui qui y a droit et à qui je le donnerai.
Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
28 Et toi, fils de l’homme, prophétise et dis: "Ainsi parle le Seigneur Dieu à l’égard des fils d’Ammon et de leurs outrages: Dis: Epée, épée dégainée, affilée pour la tuerie, pour briller comme l’éclair,
“Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
29 tandis qu’on t’adresse des prophéties vaines et des oracles de mensonge, on te pose sur le cou des cadavres des méchants dont le jour est venu, à l’heure où l’iniquité prend fin!
Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
30 Qu’elle rentre dans son fourreau! A l’endroit où tu fus créée, en ton pays d’extraction je te jugerai.
“‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
31 J’Épancherai sur, toi ma colère; le feu de ma fureur, je le soufflerai sur toi et je te livrerai dans les mains de sauvages, artisans de la destruction.
Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
32 Tu seras la proie du feu; ton sang coulera par tout le pays; on ne fera plus mention de toi, car moi, l’Eternel, j’ai parlé."
Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”

< Ézéchiel 21 >