< Exode 16 >

1 Puis ils partirent d’Èlim et arrivèrent, toute la communauté des enfants d’Israël, au désert de Sin, qui s’étend entre Elim et Sinaï; c’était le quinzième jour du deuxième mois après leur sortie du pays d’Égypte.
Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
2 Toute la communauté des enfants d’Israël murmura contre Moïse et Aaron, dans ce désert
A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
3 et les enfants d’Israël leur dirent: "Que ne sommes-nous morts de la main du Seigneur, dans le pays d’Égypte, assis près des marmites de viande et nous rassasiant de pain, tandis que vous nous avez amenés dans ce désert, pour faire mourir de faim tout ce peuple!"
Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
4 L’Éternel dit à Moïse: "Je vais faire pleuvoir pour vous une nourriture céleste, le peuple ira en ramasser chaque jour sa provision et j’éprouverai de la sorte s’il obéit à ma doctrine ou non.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
5 Le sixième jour, lorsqu’ils accommoderont ce qu’ils auront apporté, il se trouvera le double de leur récolte de chaque jour."
A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
6 Moïse et Aaron dirent à tous les enfants d’Israël: "Ce soir, vous reconnaîtrez que c’est l’Éternel qui vous a fait sortir du pays d’Égypte
Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
7 et demain, vous serez témoins de la gloire du Seigneur, lorsqu’il fera droit à vos murmures contre lui. Mais nous, que sommes nous, pour être l’objet de vos murmures?
Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
8 Vous le verrez, ajouta Moïse, lorsque Dieu vous donnera, ce soir, de la viande pour vous nourrir et demain, du pain pour vous rassasier, accueillant ainsi les murmures que vous proférez contre lui, car que sommes-nous? ce n’est pas nous qu’atteignent vos murmures, c’est l’Éternel!"
Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
9 Moïse dit à Aaron: "Dis à toute la communauté des enfants d’Israël: ‘Approchez-vous de l’Éternel, car il a entendu vos murmures.’"
Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
10 Comme Aaron parlait ainsi à toute la communauté des enfants d’Israël, ils se tournèrent du côté du désert et voici que la majesté divine apparut dans le nuage.
Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
11 L’Éternel parla ainsi à Moïse:
Ubangiji ya ce wa Musa,
12 "J’Ai entendu les murmures des Israélites. Parle-leur en ces termes: ‘Vers le soir vous mangerez de la viande, au matin vous vous rassasierez de pain et vous reconnaîtrez que moi, l’Éternel, je suis votre Dieu.’"
“Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
13 En effet, le soir, les cailles arrivèrent et couvrirent le camp et le matin, une couche de rosée s’étendait autour du camp.
Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
14 Cette couche de rosée ayant disparu, on vit sur le sol du désert quelque chose de menu, de floconneux, fin comme le givre sur la terre.
Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
15 A cette vue, les enfants d’Israël se dirent les uns aux autres: "Qu’est ceci?" car ils ne savaient ce que c’était. Et Moïse leur dit: "C’Est là le pain que l’Éternel vous donne pour nourriture.
Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
16 Voici ce qu’a prescrit l’Éternel: Recueillez-en chacun selon ses besoins: un ômer par tête; autant chacun a de personnes dans sa tente, autant vous en prendrez."
Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
17 Ainsi firent les enfants d’Israël: ils en ramassèrent, l’un plus, l’autre moins."
Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
18 Puis ils mesurèrent à l’étrier. Or, celui qui en avait beaucoup pris n’en avait pas de trop, celui qui en avait peu n’en avait pas faute, chacun avait recueilli à proportion de ses besoins.
Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
19 Moïse leur dit: "Que nul n’en réserve pour le lendemain."
Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
20 N’Écoutant point Moïse, quelques-uns gardèrent de leur provision pour le lendemain, mais elle fourmilla de vers et se gâta. Et Moïse s’irrita contre eux.
Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
21 Ils recueillirent cette substance tous les matins, chacun en raison de sa consommation; lorsque le soleil l’échauffait, elle fondait.
Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
22 Mais il advint, au sixième jour, qu’ils recueillirent une provision double, deux ômer par personne; tous les phylarques de la communauté vinrent l’annoncer à Moïse.
A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
23 Il leur répondit: "C’Est ce qu’a dit le Seigneur: Demain est le sabbat solennel, le saint chômage en l’honneur de l’Éternel! Ce que vous avez à cuire, cuisez-le, à faire bouillir, faites-le bouillir aujourd’hui et toute la provision restante, gardez-la en réserve pour demain."
Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
24 Ils la réservèrent pour le lendemain, comme l’avait ordonné Moïse et elle ne se gâta point et il ne s’y mit point de vers.
Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
25 Moïse dit: "Mangez-la aujourd’hui, car c’est aujourd’hui sabbat en l’honneur de l’Éternel, aujourd’hui vous n’en trouveriez point aux champs.
Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
26 Six jours de suite vous en recueillerez; mais le septième jour, jour de chômage, il n’y en aura point."
Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
27 Or, le septième jour, quelques-uns du peuple allèrent à la récolte, mais ils ne trouvèrent rien.
Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
28 L’Éternel dit à Moïse: "Jusqu’à quand vous refuserez-vous à garder mes préceptes et mes enseignements?
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
29 Considérez que l’Éternel vous a gratifiés du sabbat! c’est pourquoi il vous donne, au sixième jour, la provision de deux jours. Que chacun demeure où il est, que nul ne sorte de son habitation le septième jour."
Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
30 Et le peuple chôma le septième jour.
Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
31 La maison d’Israël donna à cette substance le nom de manne. Elle ressemblait à de la graine de coriandre, était blanche et avait la saveur d’un beignet au miel.
Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
32 Moïse dit: "Voici ce qu’a ordonné le Seigneur: ‘Qu’un ômer plein de cette manne reste en dépôt pour vos générations, afin qu’elles connaissent le pain dont je vous ai nourris dans le désert, lorsque je vous ai fait sortir du pays d’Égypte.’"
Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
33 Moïse dit à Aaron: "Prends une urne et y dépose un plein ômer de manne et place-la devant l’Éternel, comme souvenir pour vos générations."
Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
34 Ainsi que l’Éternel l’avait prescrit à Moïse, Aaron la déposa devant l’arche du Statut, comme souvenir.
Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
35 Les enfants d’Israël mangèrent de la manne quarante ans, jusqu’à leur arrivée en pays habité; cette manne, ils en mangèrent jusqu’à leur arrivée aux confins du pays de Canaan.
Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
36 Quant à l’ômer, c’est la dixième partie de l’êpha.
(Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)

< Exode 16 >