< Exode 10 >

1 L’Éternel dit à Moïse: "Rends toi chez Pharaon; car moi même j’ai appesanti son cœur et celui de ses serviteurs, à dessein d’opérer tous ces prodiges autour de lui
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 et afin que tu racontes à ton fils, à ton petit-fils, ce que j’ai fait aux Égyptiens et les merveilles que j’ai opérées contre eux; vous reconnaîtrez ainsi que je suis l’Éternel."
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Moïse et Aaron se rendirent chez Pharaon et lui dirent "Ainsi parle l’Éternel, Dieu des Hébreux: ‘Jusqu’à quand refuseras tu de fléchir devant moi? Laisse partir mon peuple, pour qu’il m’adore!
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 Que si tu refuses de laisser partir mon peuple, je susciterai demain des sauterelles dans ton territoire.
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 Elles déroberont la vue de la terre et l’on ne pourra plus apercevoir la terre; elles anéantiront le reste des ressources que vous a laissées la grêle, elles dévoreront toutes les plantes qui croissent pour vous dans les champs.
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 Elles rempliront tes maisons et les maisons de tous tes serviteurs et celles de toute l’Égypte: telles n’en virent point tes aïeux, ni les pères de tes aïeux, depuis le jour où ils occupèrent le pays jusqu’à ce jour.’" Et il se retira et sortit de devant Pharaon.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Les serviteurs de Pharaon lui dirent: "Combien de temps celui-ci nous portera-t-il malheur? Laisse partir ces hommes, qu’ils servent l’Éternel leur Dieu: ignores-tu encore que l’Égypte est ruinée?"
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 Moïse et Aaron furent rappelés auprès de Pharaon, qui leur dit: "Allez servir l’Éternel votre Dieu; quels sont ceux qui iront?"
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Moïse répondit: "Nous irons jeunes gens et vieillards; nous irons avec nos fils et nos filles, avec nos brebis et nos bœufs, car nous avons à fêter l’Éternel."
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 Il leur répliqua: "Ainsi soit l’Éternel avec vous, comme je compte vous laisser partir avec vos enfants! Voyez comme vos intentions sont mauvaises!
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 Non pas!… Allez, je vous prie, vous autres hommes et servez l’Éternel, puisque c’est là ce que vous désirez." Et on les chassa de devant Pharaon.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 L’Éternel dit à Moïse." Étends ta main sur le pays d’Égypte pour les sauterelles, afin qu’elles envahissent le pays d’Égypte et qu’elles dévorent tout l’herbage de la terre, tout ce qu’a épargné la grêle."
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Moïse étendit sa verge sur le pays d’Égypte; alors l’Éternel dirigea un vent d’est sur le pays tout ce jour-là, puis toute la nuit. Le matin venu, le vent d’est avait amené les sauterelles.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 Elles se répandirent, les sauterelles, par tout le pays d’Égypte et elles s’abattirent sur tout le territoire égyptien. C’Était prodigieux: pareille quantité de sauterelles ne s’était pas encore vue, pareille quantité ne devait plus se voir.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 Elles dérobèrent si complètement la vue du sol, qu’il en fut obscurci; elles dévorèrent tout l’herbage de la terre: et tous les fruits d’arbre, épargnés par la grêle et il ne resta plus de verdure soit aux arbres, soit en herbe des champs, dans tout le pays d’Égypte.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Pharaon, en toute hâte, manda Moïse et Aaron et leur dit: "J’Ai péché contre l’Éternel votre Dieu et contre vous.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 Eh bien! De grâce, pardonnez ma faute, cette fois seulement et suppliez l’Éternel votre Dieu qu’il me délivre, à tout prix, de ce fléau."
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Moïse se retira de chez Pharaon et sollicita le Seigneur.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 Et le Seigneur fit tourner le vent, qui souffla de l’ouest avec une grande violence, emporta les sauterelles et les noya dans la mer des joncs: il ne resta plus une sauterelle sur tout le territoire de l’Égypte.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 Mais l’Éternel endurcit le cœur de Pharaon et il ne renvoya pas les enfants d’Israël.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 L’Éternel dit à Moïse: "Dirige ta main vers le ciel et des ténèbres se répandront sur le pays d’Égypte, des ténèbres opaques."
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Moïse dirigea sa main vers le ciel et d’épaisses ténèbres couvrirent tout le pays d’Égypte, durant trois jours.
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 On ne se voyait pas l’un l’autre et nul ne se leva de sa place, durant trois jours mais tous les enfants d’Israël jouissaient de la lumière dans leurs demeures.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 Pharaon manda Moïse et dit: "Partez, adorez l’Éternel; seulement, que votre menu et votre gros bétail demeurent, mais vos enfants peuvent vous suivre."
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Moïse répondit: "Toi-même, tu nous donneras des victimes et des holocaustes pour les offrir à l’Éternel notre Dieu
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 et notre bétail ne nous suivra pas moins; il n’en restera pas ici un ongle, car nous devons en prendre pour sacrifier à l’Éternel notre Dieu; or, nous ne saurons de quoi lui faire hommage que lorsque nous serons arrivés."
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 Mais l’Éternel endurcit le cœur de Pharaon, qui ne consentit point à les laisser partir.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 Pharaon dit à Moïse: "Sors de devant moi! Garde-toi de reparaître à ma vue, car, le jour où tu verras mon visage, tu mourras!"
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Moïse repartit: "Tu as bien dit. Je ne reverrai plus ton visage."
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< Exode 10 >