< Amos 1 >
1 Paroles d’Amos, un des éleveurs de troupeaux à Tekoa, qui prophétisa sur Israël durant le règne d’Ouzia, roi de Juda, et de Jéroboam, roi d’Israël, deux ans avant le tremblement de terre.
Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
2 Il dit: "L’Eternel rugit de Sion, de Jérusalem il fait entendre sa voix: les pacages des bergers en sont assombris, le sommet du Carmel en est desséché."
Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
3 Ainsi parle l’Eternel: "A cause du triple, du quadruple crime de Damas, je ne le révoquerai pas, mon arrêt: parce qu’ils ont foulé le pays de Galaad avec des herses de fer.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
4 Aussi déchaînerai-je le feu contre la maison de Hazaël, pour qu’il dévore les palais de Ben-Hadad.
zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
5 Je briserai les verrous de Damas, j’exterminerai les habitants du Val de Perversité et le porte-sceptre de la maison de Délices. Le peuple d’Aram ira en exil à Kir, dit l’Eternel."
Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
6 Ainsi parle l’Eternel: "A cause du triple, du quadruple crime de Gaza, je ne le révoquerai pas, mon arrêt: parce qu’ils ont déporté des exilés en masse pour les livrer à Edom.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
7 Aussi déchaînerai-je le feu contre les murs de Gaza, pour qu’il en dévore les palais.
Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
8 J’Exterminerai les habitants d’Asdod et le porte-sceptre d’Ascalon; je dirigerai ma main contre Ekron, pour que périsse le reste des Philistins, dit le Seigneur Dieu."
Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Ainsi parle l’Eternel: "A cause du triple, du quadruple crime de Tyr, je ne le révoquerai pas, mon arrêt: parce qu’ils ont livré des captifs en masse à Edom, sans se souvenir de la fraternelle alliance.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
10 Aussi déchaînerai-je le feu contre les murs de Tyr, pour qu’il en dévore les palais."
zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
11 Ainsi parle l’Eternel: "A cause du triple, du quadruple crime d’Edom, je ne le révoquerai pas, mon arrêt: parce qu’il a poursuivi son frère avec l’épée, étouffant toute pitié; parce que sa colère ne cesse de faire des victimes, et qu’il se complaît dans une haine sans fin.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
12 Aussi déchaînerai-je le feu contre Têmân, pour qu’il dévore les palais de Boçra."
Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
13 Ainsi parle l’Eternel: "A cause du triple, du quadruple crime des fils d’Ammon, je ne le révoquerai pas, mon arrêt: parce qu’ils ont éventré les femmes enceintes de Galaad, en vue d’étendre leur territoire.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
14 Aussi mettrai-je le feu aux murs de Rabba, pour qu’il en dévore les palais, au milieu des cris de guerre, au jour du combat, au milieu de la tempête, au jour de l’ouragan.
Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
15 Malcom ira en exil, lui et ses dignitaires, tous ensemble, dit l’Eternel."
Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.