< Amos 5 >
1 Ecoutez cette parole que je prononce à votre sujet comme une complainte, ô maison d’Israël!
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 "Elle est tombée et ne peut plus se relever, la vierge d’Israël, elle est étendue sur son sol, et personne ne la redresse."
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 Oui, ainsi parle le Seigneur Dieu: "La ville qui mettait en campagne mille hommes n’en conservera que cent; celle qui mettait en campagne cent hommes n’en conservera que dix à la maison d’Israël."
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 Eh bien! ainsi parle le Seigneur à la maison d’Israël: "Recherchez-moi et vous vivrez!
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 Mais ne vous enquérez pas de Béthel, n’allez pas à Ghilgal, ne passez point à Bersabée, car Ghilgal ira en exil et Béthel deviendra une ruine.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Recherchez l’Eternel et vous vivrez! Autrement il fera éclater dans la maison de Joseph comme un feu qui dévore, sans que Béthel ait personne pour éteindre.
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 Ils changent le droit en plante vénéneuse et foulent aux pieds la justice.
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 Celui qui a créé les Pléiades et l’Orion, qui transforme les ténèbres profondes en aube matinale et fait succéder au jour la nuit sombre, qui appelle les eaux de la mer et les répand sur la surface du sol Eternel est son nom.
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 C’Est lui qui déchaîne la ruine sur les puissants, la ruine qui fond sur les forteresses.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 Ils haïssent celui qui les morigène aux portes, et ont en horreur quiconque parle avec intégrité.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Eh bien! c’est parce que vous piétinez le pauvre et lui prenez un tribut sur son blé, que vous vous bâtissez des maisons en pierres de taille: vous n’y habiterez point! Vous vous êtes planté de belles vignes: vous n’en boirez pas le vin!
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 Car je le sais bien: nombreux sont vos péchés, énormes vos crimes. Vous persécutez le juste, acceptez des présents pour léser aux portes le droit des indigents.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 C’Est pourquoi l’homme prudent se tait en ce temps-ci, car c’est un temps de malheur.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Recherchez le bien et non le mal, afin que vous viviez! Alors seulement l’Eternel, Dieu-Cebaot, sera avec vous comme vous le dites.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Haïssez le mal, aimez le bien et faites prévaloir le droit aux portes. Peut-être alors l’Eternel, Dieu-Cebaot, prendra-t-il en pitié les débris de Joseph.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 En vérité, ainsi parle l’Eternel, Dieu-Cebaot, le Seigneur: "Sur toutes les places ce seront des lamentations, dans toutes les rues on s’écriera: "Hélas! Hélas!" On conviera les laboureurs au cortège funèbre, aux démonstrations de deuil ceux qui savent des complaintes.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 Dans tous les vignobles on mènera le deuil, quand je passerai au milieu de toi, dit l’Eternel.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Malheur à qui désire voir le jour de l’Eternel! Que peut être pour vous le jour de l’Eternel? Ce sera un jour de ténèbres, non de lumière.
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 Ce sera comme quand un homme fuit devant un lion, se trouve face à face avec un ours, entre dans la maison, s’appuie contre le mur et qu’un serpent le mord.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Bien sûr, le jour de l’Eternel sera ténèbres et non lumière, il sera sombre et sans lueur.
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 Je hais, j’ai en dégoût vos fêtes, je ne prends nul plaisir à vos assemblées.
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 Quand vous m’offrez des holocaustes et des oblations, je ne les agrée point; je n’ai point de regard pour votre tribut d’animaux gras.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Faites-moi grâce du bruit de vos cantiques, que je n’entende plus le son de vos luths!
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 Mais que le bon droit jaillisse comme l’eau, la justice comme un torrent qui ne tarit point!
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Est-ce donc que vous m’avez présenté sacrifices et oblations au désert, durant quarante années, ô maison d’Israël?
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 Mais vous emporterez Siccout, votre roi, Kiyoun, votre idole, l’Etoile de votre Dieu que vous vous êtes confectionné.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 Et je vous exilerai bien au-delà de Damas, dit Celui dont le nom est Eternel, Dieu-Cebaot."
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.