< 2 Samuel 5 >

1 Toutes les tribus d’Israël vinrent auprès de David, à Hébron, et lui dirent: "Nous sommes ta chair et ton sang.
Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
2 Déjà hier, déjà avant-hier, alors que Saül était notre roi, c’est toi qui dirigeais toutes les expéditions d’Israël. C’Est toi, avait dit l’Eternel, qui gouverneras Israël, mon peuple, toi qui seras son chef…"
A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
3 Tous les anciens d’Israël vinrent donc trouver le roi, à Hébron; le roi David fit un pacte avec eux à Hébron, devant l’Eternel, et ils le sacrèrent comme roi d’Israël.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
4 David avait trente ans lorsqu’il devint roi; son règne fut de quarante ans.
Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
5 Il régna dans Hébron, sur Juda, sept ans et six mois, et dans Jérusalem il régna trentre-trois ans sur tout Israël et Juda.
A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
6 Le roi, avec ses hommes, marcha sur Jérusalem contre les Jébuséens, qui occupaient le pays; mais ceux-ci dirent à David: "Tu n’entreras pas ici que tu n’aies délogé les aveugles et les boiteux," voulant dire que David n’y entrerait point.
Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
7 Mais David s’empara de la forteresse de Sion, qui est la Cité de David.
Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
8 Ce même jour, David avait dit: "Celui qui veut battre les Jébuséens doit pénétrer jusqu’au faîte, jusqu’aux boiteux et aux aveugles", devenus odieux à David. C’Est pourquoi on a dit: "Aveugle ni boiteux ne doivent entrer dans la maison."
A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
9 David s’établit dans la forteresse, qu’il nomma la Cité de David, et ajouta des constructions tout autour, à l’intérieur du Millo:
Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
10 David alla grandissant de plus, en plus, assisté par l’Eternel, Dieu-Cebaot.
Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
11 Hiram, roi de Tyr, envoya une députation à David avec du bois de cèdre, des charpentiers et des maçons, qui bâtirent une maison pour David.
To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
12 Et David reconnut que le Seigneur l’avait destiné à régner sur Israël, et lui avait accordé une royauté glorieuse en faveur de son peuple Israël.
Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
13 David prit encore des concubines et des épouses dans Jérusalem, après son départ d’Hébron, et il lui naquit encore des fils et des filles.
Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
14 Voici les noms de ceux qui lui naquirent à Jérusalem: Chammoua, Chobab, Nathan et Salomon;
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
15 Yibhar, Elichoua, Néfeg et Yafia;
Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
16 Elichama, Elyada et Elifélet.
Elishama, Eliyada da Elifelet.
17 Les Philistins, ayant su que David avait été oint comme roi d’Israël, montèrent tous pour chercher à le prendre; David l’apprit et se rendit à la forteresse.
Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
18 Les Philistins étaient arrivés et s’étaient déployés dans la vallée de Refaïm.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
19 Alors David consulta le Seigneur en disant: "Dois-je monter vers les Philistins? Les livreras-tu en ma main?" Le Seigneur répondit à David: "Monte! Oui, je livrerai les Philistins en ta main."
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
20 David atteignit Baal-Peraçim et les y battit. Et il dit: "Le Seigneur a dispersé mes ennemis devant moi comme une eau débordée." C’Est de là que cet endroit fut nommé Baal-Peraçim.
Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
21 Ils laissèrent là leurs idoles, qui furent emportées par David et ses hommes.
Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
22 Mais de nouveau les Philistins y montèrent et se déployèrent dans la vallée de Refaïm.
Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
23 David consulta le Seigneur, qui répondit: "Ne monte pas; tourne-les par derrière et marche sur eux du côté des bekhaïm.
saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
24 Or, lorsque tu entendras un bruit de pas sur les cimes des bekhaïm, mets-toi vite en mouvement, car alors le Seigneur sera venu à ton secours pour que tu battes l’armée des Philistins."
Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
25 David se conforma aux instructions du Seigneur, et il battit les Philistins depuis Ghéba jusque vers Ghézer.
Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.

< 2 Samuel 5 >