< 2 Samuel 3 >
1 La guerre dura longtemps entre la maison de Saül et celle de David. David allait se fortifiant de plus en plus, et la maison de Saül ne cessa de s’affaiblir.
Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
2 Des fils naquirent à David à Hébron. Le premier-né fut Amnon, qu’il eut d’Ahinoam, la Jezreélite;
An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
3 son puîné Kilab, par Abigaïl, veuve de Nabal le Carmélite; le troisième, Absalon, fils de Maakha, fille de Talmaï, roi de Guechour;
na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
4 le quatrième, Adoniya, fils de Hagguit, le cinquième, Chefatia, fils d’Abital,
na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
5 et le sixième, Yitream, par Egla, femme de David. Ceux-là lui naquirent à Hébron.
na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
6 Tant que dura la guerre entre la maison de Saül et celle de David, Abner resta le soutien de la maison de Saül.
Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
7 Or, Saül avait eu une concubine nommée Riçpa, fille d’Ayya. Isboseth dit à Abner: "Pourquoi as-tu cohabité avec la concubine de mon père?"
To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
8 Abner s’irrita fort des paroles d’Isboseth, et il dit: "Suis-je une tête de chien au service de Juda? En ce moment, je fais du bien à la maison de Saül, ton père, à ses frères et à ses amis, je ne te laisse point tomber au pouvoir de David, et maintenant tu me reproches un méfait commis à l’égard de cette femme!
Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
9 Dieu m’en fasse autant et plus, à moi Abner, si je n’exécute envers David ce que le Seigneur lui a juré:
Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
10 d’enlever la royauté à la maison de Saül et d’établir le trône de David sur Israël et sur Juda, depuis Dan jusqu’à Bersabée!"
Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
11 Il ne put répondre un seul mot à Abner, par suite de la crainte qu’il lui inspirait.
Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
12 Alors Abner envoya des messagers à David pour décider, en son nom, à qui appartiendrait le pays, en disant: "Fais ton traité avec moi, et je te prêterai main-forte pour rallier autour de toi tout Israël.
Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
13 Bien, répondit-il, je veux faire un pacte avec toi; mais je te demande une chose, savoir: que tu ne viennes pas me voir, sinon en m’amenant Mikhal, fille de Saül, quand tu te présenteras devant moi."
Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
14 Et David envoya des messagers à Isboseth, fils de Saül, pour lui dire: "Restitue ma femme, Mikhal, que j’ai obtenue comme épouse au prix de cent prépuces de Philistins."
Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
15 Isboseth envoya pour la faire ramener de chez le mari de chez Paltiel, fils de Laïch.
Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
16 Son mari l’accompagna en pleurant et la suivant jusqu’à Bahourim; là, Abner lui dit: "Retourne sur tes pas", et il s’en retourna.
Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
17 Abner s’aboucha avec les anciens d’Israël, en disant: "Depuis longtemps vous avez demandé que David devint votre roi.
Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
18 Maintenant donc, agissez, car l’Eternel a dit au sujet de David: C’Est par la main de mon serviteur David que je veux délivrer mon peuple Israël de la puissance des Philistins et de tous ses ennemis."
To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
19 Abner fit aussi entendre ses paroles aux Benjamites, puis il se rendit à Hébron pour faire connaître à David ce qui avait été agréé d’Israël et de toute la maison de Benjamin.
Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
20 Abner arriva donc auprès de David à Hébron, accompagné de vingt hommes; David donna un festin à Abner et aux hommes qui l’accompagnaient.
Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
21 Et Abner dit à David: "Je vais, de ce pas, convoquer tous les Israélites auprès de mon seigneur le roi, afin qu’ils concluent un pacte avec toi, et tu régneras partout où il te plaira." Et David congédia Abner, qui s’en alla en paix.
Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
22 Cependant Joab, avec les serviteurs de David, revenait d’une expédition, rapportant un butin considérable. Abner n’était plus à Hébron avec David, qui l’avait congédié et laissé partir en paix.
Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
23 Joab, avec toute la troupe qui l’accompagnait, étant survenu, on annonça à Joab qu’Abner, fils de Ner, était arrivé auprès du roi et que celui-ci l’avait congédié et laissé partir en paix.
Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
24 Joab alla trouver le roi et lui dit: "Qu’as-tu fait? Abner est venu auprès de toi, pourquoi donc l’as-tu congédié et a-t-il pu s’en aller?
Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
25 Tu connais Abner, fils de Ner; il n’est venu que pour te tromper, pour connaître tes allées et venues, pour savoir tout ce que tu fais!"
Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
26 Et Joab, étant sorti de chez David, envoya des messagers sur les pas d’Abner, et ils le ramenèrent de la citerne de Sire, à l’insu de David.
Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
27 Abner rebroussa donc chemin vers Hébron; Joab l’entraîna vers l’intérieur de la porte comme pour lui parler en secret; il le frappa à l’aine et le fit ainsi mourir, pour venger le sang de son frère Assahel.
To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
28 David, l’ayant appris plus tard, dit: "Je suis innocent devant Dieu à jamais, moi et ma dynastie, du sang d’Abner, fils de Ner.
Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
29 Qu’il pèse sur la tête de Joab et de tous les siens! Qu’il ne cesse d’y avoir, dans sa famille, des gens affligés de flux ou de lèpre, s’appuyant sur des béquilles, victimes de l’épée ou manquant de pain!"
Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
30 Or, Joab et son frère Abisaï avaient tué Abner, parce qu’il avait fait périr Assahel, leur frère, à Gabaon, pendant la guerre.
(Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
31 David dit à Joab et à tout le peuple qui l’accompagnait: "Déchirez vos vêtements, ceignez-vous de cilices et lamentez-vous devant le corps d’Abner." Pour le roi David, il marchait derrière le cercueil.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
32 Abner fut enseveli à Hébron; le roi, élevant la voix, sanglota près de sa tombe; tout le peuple aussi pleura.
Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
33 Et le roi prononça cette élégie sur Abner: "Abner devait-il mourir de la mort d’un indigne!
Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
34 Tes mains n’avaient pas été liées, ni tes pieds engagés dans des chaînes: tu es tombé comme on tombe devant, les enfants du crime!" Et les pleurs du peuple entier redoublèrent.
Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
35 Le peuple voulut faire: prendre de la nourriture à David, encore en plein jour; mais David jura en disant: "Que Dieu me punisse autant et plus, si je goûte du pain ou quoi que ce soit avant le coucher du soleil!"
Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
36 Tout le peuple en eut connaissance et cela leur plut, comme plaisait au peuple tout ce que faisait le roi.
Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
37 Tout le peuple, tout Israël comprit alors que le meurtre d’Abner, fils de Ner, n’était pas imputable au roi.
Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
38 Le roi dit à ses serviteurs: "Vous savez bien qu’un prince et un grand homme est tombé aujourd’hui en Israël.
Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
39 Pour moi, je suis faible encore et viens d’être sacré roi, et ces hommes, les fils de Cerouya, sont plus forts que moi. A Dieu de punir le méchant selon sa méchanceté!"
A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”