< 2 Rois 3 >

1 Joram, fils d’Achab, monta sur le trône d’Israël, à Samarie, la dix-huitième année du règne de Josaphat, roi de Juda; il régna douze ans.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Il fit ce qui déplaît aux yeux de l’Eternel, toutefois, moins que son père et que sa mère; c’est ainsi qu’il fit enlever la statue de Baal érigée par son père.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Mais il suivit, sans s’en écarter, les voies perverses de Jéroboam, fils de Nebat, qui avait induit Israël au péché.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Mécha, roi de Moab, était riche en troupeaux: il payait au roi d’Israël un tribut de cent, mille agneaux et de cent mille béliers pourvus de leur laine.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 Mais à la mort d’Achab, le roi de Moab fit défection au roi d’Israël.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Aussitôt, Joram quitta Samarie et passa en revue tout Israël.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 Puis il se décida à envoyer le message suivant à Josaphat, roi de Juda: "Le roi de Moab s’est révolté contre moi. Veux-tu aller en guerre avec moi contre Moab?" Il répondit: "J’Irai; toi et moi, ton peuple et mon peuple, tes chevaux et les miens, c’est tout un.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Quel chemin prendrons-nous? demanda Joram. La route du désert iduméen," répondit Josaphat.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Le roi d’Israël, le roi de Juda et le roi d’Edom entrèrent donc en campagne. Mais, après sept jours de marche, l’eau manqua aux troupes et aux bêtes qui les suivaient.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Le roi d’Israël s’écria: "Hélas! Est-ce que l’Eternel aurait fait appel à ces trois rois pour les livrer aux mains de Moab!"
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Josaphat dit: "N’Y a-t-il point ici de prophète de Dieu auprès de qui nous puissions consulter le Seigneur?" Un des serviteurs du roi d’Israël répondit: "Il se trouve ici Elisée, fils de Chefat, qui a versé l’eau sur les mains d’Elie.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 La parole divine est sur ses lèvres, dit Josaphat." Le roi d’Israël, Josaphat et le roi d’Edom se rendirent donc auprès de lui.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Mais Elisée apostropha ainsi le roi d’Israël: "Qu’y a-t-il de commun entre toi et moi? Adresse-toi aux prophètes de ton père et aux prophètes de ta mère." Le roi d’Israël répondit: "Laissons cela. Est-ce que l’Eternel a fait appel à ces trois rois pour les livrer aux mains de Moab?"
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Elisée reprit: "Vive l’Eternel-Cebaot, que je sers! Si je ne respectais la personne de Josaphat, roi de Juda, je ne t’accorderais pas même un regard.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Eh bien! Amenez-moi un musicien." Tandis que celui-ci jouait de son instrument, l’esprit du Seigneur s’empara du prophète,
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 et il dit: "Ainsi a parlé l’Eternel: Creusez dans cette vallée fossés et fossés.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Car (telle est la parole de l’Eternel), vous ne sentirez pas de vent et vous ne verrez pas de pluie, et cependant cette vallée sera remplie d’eau, et vous aurez à boire, vous, vos troupeaux et vos bêtes.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Mais c’est encore trop peu aux yeux de l’Eternel: il livrera aussi Moab en votre pouvoir.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 Vous détruirez toute ville forte, toute ville de marque; vous abattrez tout arbre fruitier, vous comblerez toute source d’eau, et toute bonne terre, vous la ruinerez en la couvrant de pierres."
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Le lendemain matin, à l’heure de l’oblation, l’eau arriva tout à coup du côté d’Edom, et le sol en fut inondé.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Tous les Moabites, ayant appris que les rois venaient porter la guerre chez eux, s’étaient rassemblés en armes, tous les hommes en âge de ceindre l’épée et au delà et s’étaient postés sur la frontière.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 S’Étant levés au matin, comme le soleil brillait au-dessus des eaux, celles-ci apparurent dé loin aux Moabites rouges comme du sang.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 Ils s’écrièrent: "C’Est du sang! Assurément, les rois se sont pris de querelle, ils se sont entr’égorgés: au butin donc, Moab!"
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Ils se précipitèrent sur le camp des Israélites, mais ceux-ci se levèrent, battirent les Moabites, les mirent en fuite et en firent un grand carnage:
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 Ils détruisirent les villes; chacun lança sa pierre sur les terres fertiles, qui en furent couvertes; ils comblèrent les sources et abattirent les arbres fruitiers. Il ne resta pierre sur pierre qu’à Kir-Haréset, qui fut assaillie, à son tour, de tous côtés par les frondeurs et ruinée.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Le roi de Moab, se voyant trop faible pour lutter, se mit à la tête de sept cents hommes, l’épée nue, afin de se frayer un chemin jusqu’au roi d’Edom; mais ils n’y réussirent point.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Alors il prit l’aîné de ses fils, l’héritier du trône, et l’immola en holocauste au haut des remparts. Aussitôt, une grande colère éclata contre Israël, qui dut se retirer et rentrer dans son pays.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< 2 Rois 3 >