< 2 Rois 2 >

1 Quand l’Eternel fit monter Elie au ciel dans un tourbillon, Elle et Elisée quittaient Ghilgal.
Da lokaci ya yi da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa sama cikin guguwa, Iliya da Elisha kuwa suna kan hanyarsu daga Gilgal.
2 Elie dit à Elisée: "Reste ici, de grâce, car l’Eternel m’a donné une mission pour Béthel. Vive Dieu et par ta propre vie! répondit Elisée, je ne te quitterai pas." Et ils se rendirent ensemble à Béthel.
Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka dakata a nan; Ubangiji ya aike ni Betel.” Amma Elisha ya amsa ya ce, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka gangara zuwa Betel.
3 Les jeunes prophètes établis à Béthel allèrent au-devant d’Elisée et lui dirent: "Sais-tu que l’Eternel t’enlève aujourd’hui ton maître, ton guide?" Il répondit: "Silence, oui, je le sais."
Sai ƙungiyar annabawa a Betel suka fito zuwa wajen Elisha suka ce masa, “Ka san cewa Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga wurinka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma kada ku yi magana game da wannan.”
4 Elie reprit: "Elisée, reste ici, car l’Eternel m’a confié une mission pour Jéricho. Vive l’Eternel, répliqua-t-il, et par ta propre vie! Je ne te quitterai pas." Et ils vinrent ensemble à Jéricho.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan Elisha; Ubangiji ya aike ni Yeriko.” Sai ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai ma kana a raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka sai suka tafi Yeriko.
5 Les jeunes prophètes établis à Jéricho se rendirent auprès d’Elisée et lui dirent: "Sais-tu que l’Eternel t’enlève aujourd’hui ton maître, ton guide? Silence, répondit-il, oui, je le sais."
Ƙungiyar annabawa a Yeriko suka haura zuwa wajen Elisha suka ce, “Ko ka san Ubangiji zai ɗauki maigidanka daga gare ka yau?” Sai ya ce, “I, na sani, amma ku bar zancen nan tukuna.”
6 Et Elie dit de nouveau: "Reste ici, je te prie, car l’Eternel m’envoie du côté du Jourdain." Il répondit: "Vive l’Eternel et par ta propre vie! Je ne te quitterai pas." Et ils continuèrent ensemble leur route.
Sai Iliya ya ce masa, “Ka dakata a nan, Ubangiji ya aike ni Urdun.” Sai Elisha ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, kai kuma kana raye, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka ci gaba da tafiya tare.
7 Cinquante jeunes prophètes allèrent, de leur côté, et se placèrent en vue d’eux à une certaine distance; les deux prophètes s’étaient arrêtés près du Jourdain.
Mutum hamsin na ƙungiyar annabawa suka je suka tsaya da nisa, suna fuskantar inda Iliya da Elisha suka tsaya a Urdun.
8 Elie prit son manteau, le roula, en frappa les eaux, qui se séparèrent en deux, et ils passèrent ensemble à pieds secs.
Sai Iliya ya tuɓe rigarsa, ya nannaɗe ya bugi ruwan Urdun da shi. Sai ruwan ya dāre gida biyu, suka haye a busasshiyar ƙasa.
9 Pendant qu’ils traversaient, Elie dit à Elisée: "Exprime un désir; que puis-je faire pour toi avant que je te sois enlevé?" Elisée répondit: "Puissé-je avoir une double part de l’esprit qui t’inspire!
Da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Faɗi mini, abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga gare ka!” Elisha ya amsa ya ce, “Bari in gāji ninki biyu na ruhunka.”
10 Tu as demandé quelque chose de difficile, répondit Elie; tu seras cependant satisfait si tu me vois disparaître à tes yeux, mais sinon, non."
Iliya ya ce, “Ka nemi abu mai wuya, amma in ka ga lokacin da aka ɗauke ni daga gare ka, zai zama naka, in ba haka ba, ba za ka samu ba ke nan.”
11 Ils, poursuivaient leur chemin en conversant, quand tout à coup un char de feu, attelé de chevaux de feu, les sépara l’un de l’autre, et Elie monta au ciel dans un tourbillon.
Yayinda suke tafiya suna magana, sai kwatsam, keken yaƙin wuta da dawakan wuta suka ratse tsakaninsu, sai Iliya ya tafi sama a cikin guguwa.
12 A cette vue, Elisée s’écria: "Mon père, mon père! Char et cavalerie d’Israël!" Et il ne le vit plus. Alors il saisit ses vêtements, et les déchira de part en part.
Da Elisha ya ga haka sai ya yi ihu yana cewa, “Babana! Babana! Kekunan yaƙin da mahayan dawakan Isra’ila!” Elisha kuwa bai sāke ganinsa ba. Sai ya kama tufafinsa ya yayyage.
13 Puis il ramassa le manteau qui était tombé des épaules d’Elie, et retourna sur les rives du Jourdain, où il s’arrêta.
Sai ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya koma ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun.
14 Il prit le manteau qui était tombé des épaules d’Elie, et en frappa les eaux en s’écriant: "Où est l’Eternel, le Dieu d’Elie?" et sous ses coups les eaux se séparèrent devant lui également, et il passa.
Sa’an nan Elisha ya ɗauki rigar da ta fāɗo daga Iliya ya bugi ruwan da shi. Ya ce, “Yanzu ina Ubangiji Allah na Iliya?” Da ya bugi ruwan sai ruwan ya dāre gida biyu, sai ya haye.
15 Les jeunes prophètes de Jéricho avaient vu de loin ce qui s’était passé, et ils dirent: "L’Esprit d’Elie repose sur Elisée." Ils allèrent à sa rencontre, et se prosternèrent devant lui jusqu’à terre.
Ƙungiyar annabawa daga Yeriko, waɗanda suke kallo, suka ce, “Ruhun Iliya yana a kan Elisha.” Sai suka je su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa.
16 Ils lui dirent: "Il y a parmi tes serviteurs cinquante hommes vaillants: laisse-les donc aller à la recherche de ton maître. Peut-être le souffle de l’Eternel l’a-t-il emporté et jeté sur une des montagnes, ou dans une des vallées. N’Envoyez personne," répliqua-t-il.
Suka ce, “Duba, mu bayinka muna da masu ji da ƙarfi hamsin. Bari su je su nemi maigidanka. Wataƙila, Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi ya ajiye bisa wani dutse, ko wani kwari.” Elisha ya ce, “A’a, kada ku aike su.”
17 Mais ils insistèrent au point de l’embarrasser, et il dit: "Envoyez!" Ils envoyèrent cinquante hommes, qui cherchèrent le prophète pendant trois jours, mais sans le trouver.
Amma suka matsa masa har ya ji ba ya iya hana su. Saboda haka ya ce, “Ku aike su.” Sai suka aiki mutane hamsin, suka yi ta nema har kwana uku amma ba su same Iliya ba.
18 Quand ils revinrent auprès d’Elisée, qui était resté à Jéricho, il leur dit: "Ne vous avais-je pas conseillé de ne pas aller?"
Da suka dawo wurin Elisha, wanda yake a Yeriko, sai ya ce musu, “Ban ce muku kada ku tafi ba?”
19 Or, les habitants de Jéricho dirent à Elisée: "Le séjour de cette ville est agréable, comme mon seigneur le voit; mais l’eau y est malsaine et le sol meurtrier."
Mutane garin suka ce wa Elisha, “Ranka yă daɗe, duba, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba shi da kyau, ƙasar kuma ba ta ba da amfani.”
20 Il répondit: "Apportez-moi une cruche neuve que vous remplirez de sel;" et on la lui apporta.
Sai ya ce, “Ku kawo mini sabuwar ƙwarya, ku kuma sa gishiri a ciki.” Sai suka kawo masa.
21 Il alla vers la source d’où venait l’eau et y jeta le sel en disant: "Telle est la parole de l’Eternel: Je vais rendre ces eaux salubres, et elles ne causeront plus ni mort ni ravages."
Sai ya tafi maɓulɓular ruwan yana watsa gishirin a ciki, yana cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da ruwan nan. Ba zai ƙara jawo mutuwa, ko yă hana ƙasar ba da amfani ba.’”
22 Les eaux devinrent salubres, jusqu’au jour présent, selon la prédiction faite par Elisée.
Ruwan ya tsabtacce har yă zuwa yau, bisa ga faɗin Elisha.
23 Il se rendit de là à Béthel. Il suivait la montée, quand de jeunes garçons, sortant de la ville, l’insultèrent en ces termes: "Monte, chauve, monte, chauve!"
Daga nan sai Elisha ya tafi Betel. Yayinda yake tafiya a hanya, sai waɗansu matasa suka fito daga cikin gari, suka yi masa dariya suna cewa, “Ka haura, ya kai mai kai marar gashi! Ka haura, kai mai kai marar gashi!”
24 Il se retourna pour les voir, et les maudit au nom de l’Eternel. Aussitôt, deux ours sortirent de la forêt et mirent en pièces quarante-deux de ces enfants.
Sai ya juya ya dube su, ya la’anta su da sunan Ubangiji. Sai beyar guda biyu suka fito daga jeji suka hallaka matasa arba’in da biyu daga cikinsu.
25 De là, il se dirigea vers le mont Carmel, d’où il revint à Samarie.
Sai ya ci gaba zuwa Dutsen Karmel, daga can kuma ya koma Samariya.

< 2 Rois 2 >