< 2 Rois 12 >

1 Il monta sur le trône dans la septième année de Jéhu, et il régna quarante ans à Jérusalem. Sa mère s’appelait Cibya, de Beersabée.
A shekara ta bakwai ta Yehu, Yowash ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima na tsawon shekaru arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; daga Beyersheba.
2 Joas fit toute sa vie ce qui plaît au Seigneur, conformément aux enseignements que lui avait donnés le prêtre Joïada.
Yowash ya aikata abin da yake daidai a idon Ubangiji domin Yehohiyada firist ya koya masa.
3 Seulement, les hauts-lieux ne disparurent point; le peuple continuait d’offrir des sacrifices et de l’encens sur les hauts-lieux.
Amma fa ba a kawar da masujadan kan tuddai ba; mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da kuma ƙona turare a kan tuddai.
4 Joas dit aux prêtres: "Tout l’argent consacré qu’on apporte dans la maison de Dieu, l’argent donné par chaque homme qui est recensé ainsi que celui qui est versé pour l’estimation des personnes, et toutes les sommes que chacun, suivant l’impulsion de son cœur, offrira au temple.
Yowash ya ce wa firistoci, “Ku tattara dukan kuɗin da ake kawo a matsayin hadayu masu tsarki na haikalin Ubangiji, kuɗin da aka tattara a ƙidaya, kuɗin da aka tattara daga wa’adin da mutum ya yi, da kuma kuɗin da aka kawo na yardan rai a haikali.
5 que les prêtres les prennent, chacun des gens de sa connaissance, et qu’ils réparent eux-mêmes les dégradations du temple, partout où il s’en trouvera."
Bari kowane firist yă karɓi kuɗi daga masu ajiya, sa’an nan a yi amfani da su a gyara duk wani abin da ya lalace a haikali.”
6 Or, dans la vingt-troisième année du règne de Joas, les prêtres n’avaient pas encore réparé les dégradations du temple.
Amma har zuwa shekara ta ashirin da uku ta mulkin Yowash, firistocin ba su yi gyara haikalin ba.
7 Joas manda alors le pontife Joïada et les autres prêtres et leur dit: "Pourquoi ne réparez-vous pas les dégradations du temple? Dorénavant, n’acceptez plus d’argent de vos connaissances, mais affectez-le aux réfections du sanctuaire."
Saboda haka Sarki Yowash ya kira Yehohiyada firist da sauran firistoci ya tambaye su ya ce, “Me ya sa ba kwa gyaran abubuwan da suka lalace a haikali? Kada ku sāke karɓan kuɗi daga masu ajiya, amma a miƙa su domin gyaran haikali.”
8 Les prêtres convinrent de ne plus recevoir d’argent du peuple et de ne pas s’occuper des réparations du temple.
Firistoci suka yarda cewa ba za su sāke karɓan kuɗi daga mutane ba, kuma ba za su yi gyaran haikalin da kansu ba.
9 Joïada le prêtre, prit une caisse, perça un trou dans le couvercle, et la plaça à côté de l’autel, à droite de l’entrée du temple, et les prêtres préposés à la garde du seuil y jetaient tout l’argent qu’on apportait dans la maison de Dieu.
Yehohiyada firist ya ɗauki akwatin ya huda rami a murfinsa. Ya ajiye shi kusa da bagade a hannun dama na haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka zuba dukan kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji a cikin akwatin.
10 Lorsqu’ils voyaient que l’argent était abondant dans la caisse, le secrétaire du roi et le grand prêtre allaient ramasser et compter la somme qui se trouvait dans le temple de l’Eternel.
Duk sa’ad da suka ga kuɗin sun ƙaru a akwatin, sai marubucin fada da babban firist, su ƙirga kuɗin da aka kawo a haikalin Ubangiji su sa a jakankuna.
11 Ils remettaient ensuite l’argent ainsi compté à ceux qui étaient chargés des travaux du temple, et ceux-ci le dépensaient en payant les charpentiers et les architectes qui travaillaient à la maison de Dieu,
Sa’ad da suka ga kuɗin ya yi yawa, sai su ba wa waɗanda aka zaɓa su lura da aikin haikalin. Da shi suka biya waɗanda suka yi aiki a haikalin Ubangiji, su kafintoci, da magina,
12 ainsi que les maçons et les tailleurs de pierres, et en achetant le bois et les pierres de taille nécessaires aux réparations de la maison de Dieu, enfin pour toute dépense nécessitée par la restauration du temple.
masu gini, da masu fasa duwatsu. Suka sayi katakai da sassaƙaƙƙun duwatsu domin gyaran haikalin Ubangiji, suka kuma biya duk waɗansu kuɗin gyaran haikalin.
13 Cependant, on ne confectionnait pour la maison de Dieu ni bassins d’argent, ni couteaux, ni cuvettes, ni trompettes, ni aucun ustensile d’or et d’argent, avec les sommes apportées au temple.
Ba a yi amfani da kuɗin da aka kawo a haikali don yin manyan kwanonin azurfa, lagwani, abin yayyafa ruwa, kakaki ko wani abu na zinariya, ko na azurfa domin haikalin Ubangiji ba;
14 Elles étaient remises aux directeurs des travaux, qui les consacraient aux réparations de la maison de Dieu.
an ba ma’aikatan da suka gyara haikalin ne.
15 On ne demandait pas de comptes aux hommes à qui l’on confiait l’argent pour le remettre aux ouvriers, car ils agissaient avec honnêteté.
Ba su bukaci wani bayani daga waɗanda aka ba wa kuɗin don su biya ma’aikatan ba, domin sun yi aikinsu da aminci.
16 L’Argent provenant des sacrifices délictifs ou expiatoires n’était pas apporté au temple: il appartenait aux prêtres.
Ba a kawo kuɗi daga hadayun laifi da na hadayun zunubi a haikalin Ubangiji ba, waɗannan na firistoci ne.
17 En ce temps-là, Hazaël, roi de Syrie, alla attaquer Gath et s’en empara; puis il se prépara à monter vers Jérusalem.
A wannan lokaci, Hazayel sarkin Aram ya haura, ya kai wa Gat hari, ya kuma ci ta da yaƙi. Sa’an nan ya juya don yă yaƙi Urushalima.
18 Joas roi de Juda, prit tous les objets consacrés par Josaphat, Joram et Achazia, ses aïeux, qui avaient régné sur Juda, avec les objets qu’il avait consacrés lui-même, ainsi que tout l’or contenu dans les trésors du temple, et il les fit remettre à Hazaël, roi de Syrie. Celui-ci s’éloigna alors de Jérusalem.
Amma Yowash sarkin Yahuda ya kwashe tsarkakan kayan da kakanninsa, Yehoshafat, Yehoram da Ahaziya, sarakunan Yahuda suka keɓe, da kyautai da shi kansa ya keɓe, da kuma dukan azurfan da aka samu a ɗakunan ajiya haikalin Ubangiji da na fada, ya aika da su wa Hazayel sarkin Aram, shi kuma ya janye daga Urushalima.
19 Pour le reste de l’histoire et des actes de Joas, ils sont consignés dans le livre des annales des rois de Juda.
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
20 Les serviteurs de Joas, en révolte contre lui, avaient formé un complot et l’avaient frappé dans la maison de Millo, sur le chemin qui descend vers Silla.
Hafsoshinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a Bet Millo, a kan hanyar da ta gangara zuwa Silla.
21 C’Étaient ses serviteurs Yozakhar, fils de Chimeat, et Yehozabad, fils de Chomer, qui l’avaient frappé à mort; il fut inhumé avec ses pères dans la Cité de David, et eut pour successeur son fils Amacia.
Hafsoshin da suka kashe shi kuwa su ne Yozabad ɗan Shimeyat da Yehozabad ɗan Shomer. Ya mutu, aka kuma binne shi tare da kakanninsa a Birnin Dawuda. Sai Amaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Rois 12 >