< 2 Rois 11 >

1 Athalie, mère d’Achazia, voyant son fils mort, se mit à exterminer toute la race royale.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 Mais Josabeth, fille du roi Joram et sœur d’Achazia, se saisit de Joas, fils d’Achazia, l’arracha furtivement d’entre les fils du roi, qui avaient été mis à mort, l’installa, lui et sa nourrice, dans la chambre des lits. On le déroba aux regards d’Athalie, et ainsi il échappa à la mort.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 Il resta avec elle dans le temple de l’Eternel, se tenant caché pendant six ans, tandis qu’Athalie régnait sur le pays.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 La septième année, Joïada envoya convoquer les centeniers des Cariens et des gardes et les fit entrer près de lui dans le temple de l’Eternel. Il conclut un pacte avec eux et leur fit prêter serment dans la maison de l’Eternel; puis il leur montra le fils du roi.
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 Il leur donna les instructions suivantes: "Voici ce que vous ferez: un tiers d’entre vous, de ceux qui prennent la semaine, montera la garde à la maison du roi,
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 un tiers à la porte de Sour et un tiers à la porte placée derrière les coureurs; vous exercerez votre surveillance sur la maison, du côté de l’entrée.
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 Deux sections, composées de tous ceux qui quittent le service de la semaine, monteront la garde au temple de l’Eternel, à la disposition du roi.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 Vous ferez cercle autour du roi, les armes à la main, et quiconque voudra fendre les rangs sera mis à mort; vous accompagnerez le roi dans toutes ses démarches."
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 Les centeniers exécutèrent fidèlement les ordres donnés par Joïada, le prêtre; ils prirent chacun leurs hommes, ceux qui commençaient et ceux qui avaient fini la semaine, et ils vinrent près de Joïada, le prêtre.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 Le prêtre délivra aux centeniers les lances et les boucliers déposés par David dans le temple de l’Eternel.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 Les gardes, armes en main, rangés en partant du côté droit jusqu’au côté gauche du temple, devant l’autel et le sanctuaire, entouraient le roi.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 Joïada fit sortir le fils du roi et lui remit la couronne et le "témoignage"; on le proclama roi, on l’oignit, et, au milieu des applaudissements, on cria: "Vive le roi!"
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 Athalie, entendant la voix des gardes et du peuple, accourut au milieu de la foule dans le temple de l’Eternel.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 Elle regarda et vit ce spectacle: le roi debout sur l’estrade selon l’usage, les chefs et les trompettes acclamant le roi, toute la foule manifestant sa joie en sonnant de la trompette. A cette vue, Athalie déchira ses vêtements et s’écria: "Trahison, trahison!"
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 Joïada, le pontife, adressa aux centeniers qui commandaient les troupes l’ordre suivant: "Faites-la sortir des rangs, et qui la suivra, qu’on l’exécute avec le glaive!" Car le pontife avait recommandé qu’elle ne fût pas mise à mort dans la maison de l’Eternel.
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 On fit place devant elle, et elle prit le chemin de l’entrée des chevaux pour se rendre au palais royal; là, elle fut mise à mort.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 Joïada conclut un pacte entre l’Eternel, le roi et le peuple, celui-ci devenant le peuple de l’Eternel, et entre le roi et le peuple.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 Toute la foule pénétra dans le temple de Baal et le saccagea; on brisa complètement ses autels et ses statues, on tua devant les autels Mâtan, prêtre de Baal. Le pontife plaça des surveillants dans la maison de l’Eternel.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 Sur son ordre, les centeniers, les Cariens, les gardes et les gens du peuple conduisirent le roi de la maison de l’Eternel, par le chemin de la porte des gardes, au palais royal; là, il s’assit sur le trône des rois.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 Tout le peuple se réjouit et la ville retrouva le calme. Quant à Athalie, on l’avait fait mourir par le glaive dans le palais royal.
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 Joas avait sept ans quand il devint roi.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.

< 2 Rois 11 >