< 2 Chroniques 7 >

1 Lorsque Salomon eut terminé sa prière, le feu descendit du ciel, consuma l’holocauste et les autres sacrifices, et la gloire de l’Eternel remplit la maison.
Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
2 Les prêtres ne purent entrer dans la maison du Seigneur, parce que la majesté divine remplissait cette maison du Seigneur.
Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
3 Tous les enfants d’Israël, à la vue du feu descendu du ciel et de la gloire de l’Eternel reposant sur la maison, se mirent à genoux sur les dalles, la face contre terre, se prosternèrent et rendirent hommage au Seigneur, en chantant: "Car il est bon, car sa grâce est éternelle!"
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
4 Le roi Salomon et tout le peuple offrirent des sacrifices devant le Seigneur.
Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
5 Quant aux sacrifices qu’immola le roi Salomon, ils consistèrent en vingt-deux mille taureaux et cent vingt mille brebis. Ainsi fut inaugurée la maison de Dieu par le roi et tout le peuple.
Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
6 Les prêtres se tenaient à leur poste ainsi que les Lévites, qui étaient munis des instruments de musique sacrée, créés par le roi David, et rendaient hommage au Seigneur, en chantant: "Car sa grâce est éternelle!" d’après le cantique de David confié à leurs soins. Les prêtres sonnaient de la trompette en face d’eux, et tous les Israélites étaient debout.
Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
7 Salomon consacra l’intérieur du parvis, qui s’étend devant la maison du Seigneur, pour qu’on pût y offrir les holocaustes et les parties grasses des rémunératoires; car l’autel de cuivre construit par Salomon ne pouvait contenir à la fois holocaustes, oblations et graisses.
Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
8 En ce temps-là, Salomon célébra la fête de Souccot durant sept jours, tout Israël étant avec lui, une assemblée extrêmement nombreuse accourue, depuis Hemath jusqu’au torrent d’Egypte.
Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
9 Le huitième jour on fit une fête de clôture. En effet, on avait procédé à la dédicace de l’autel pendant sept jours et célébré la fête de Souccot pendant sept jours.
A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
10 Le vingt-troisième jour du septième mois, Salomon renvoya dans ses foyers le peuple, heureux et le cœur réjoui de toutes les grâces dont le Seigneur avait comblé David, Salomon et Israël, son peuple.
A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
11 Salomon acheva ainsi la maison du Seigneur et la demeure royale; il accomplit heureusement tout ce qu’il avait projeté de faire pour la maison du Seigneur et pour son propre palais.
Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
12 Alors le Seigneur apparut à Salomon pendant la nuit, et lui dit: "J’Accueille ta prière, et je fais choix de cette maison comme d’un lieu de sacrifices.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
13 S’Il arrive que je ferme le ciel pour qu’il n’y ait point de pluie, que j’ordonne aux sauterelles de ravager le pays ou que je déchaîne une épidémie contre mon peuple,
“Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
14 et qu’alors mon peuple, auquel mon nom se trouve associé, s’humilie, m’adresse des prières, recherche ma présence et abandonne ses mauvaises voies, à mon tour je l’exaucerai du haut du ciel, lui pardonnerai ses péchés et réparerai les ruines de son pays.
in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
15 Dès à présent, mes yeux seront ouverts et mes oreilles attentives aux prières prononcées en ce lieu.
Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
16 Dès à présent aussi, je choisis et sanctifie cette maison en y faisant régner mon nom à jamais, en y dirigeant constamment mes yeux et ma pensée.
Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
17 Pour toi, si tu marches devant moi comme a marché David, ton père, en te conformant à tout ce que je t’ai prescrit, en gardant mes lois et mes statuts,
“Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
18 je maintiendrai le trône de ta royauté, en vertu du pacte que j’ai fait avec ton père David, en disant: "Jamais il ne manquera un des tiens pour régner sur Israël."
zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
19 Mais si vous vous égarez, si vous délaissez mes lois et mes préceptes que je vous ai donnés, et que vous alliez servir des dieux étrangers et vous prosterner devant eux,
“Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
20 je vous arracherai du pays que je vous avais donné; cette maison, que j’ai consacrée à mon nom, je la répudierai et j’en ferai la fable et la risée de toutes les nations;
zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
21 et cette maison placée à un si haut rang ne produira plus que stupeur chez tout venant; et quand on dira: "Pourquoi le Seigneur a-t-il traité ainsi ce pays et ce temple?"
Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
22 On répondra: "Parce qu’ils ont abandonné le Seigneur, Dieu de leurs pères, qui les avait délivrés de l’Egypte, ont adopté des divinités étrangères, les ont servies et adorées, c’est pour cela que le Seigneur a fait fondre sur eux tous ces malheurs."
Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”

< 2 Chroniques 7 >