< 2 Chroniques 31 >

1 Quand tout cela fut terminé, tous les Israélites qui se trouvaient là s’en allèrent par les villes de Juda; ils brisèrent les statues, abattirent les Achêra, démolirent les hauts lieux et les autels dans tout Juda, Benjamin, Ephraïm et Manassé, jusqu’à complète destruction, et tous les enfants d’Israël s’en retournèrent chacun chez soi, dans leurs villes.
Sa’ad da aka gama dukan wannan, sai Isra’ilawan da suke can suka fita zuwa garuruwan Yahuda, suka rurrushe keɓaɓɓun duwatsu suka kuma farfashe ginshiƙan Ashera. Suka rurrushe masujadan kan tudu da bagadai, ko’ina a Yahuda da Benyamin da kuma cikin Efraim da Manasse. Bayan sun rurrushe dukansu, sai Isra’ilawa suka koma garuruwansu, kowanne zuwa mahallinsa.
2 Ezéchias établit les classes de prêtres et de Lévites selon leurs divisions, chacun selon son service, prêtres et Lévites, pour les holocaustes et les rémunératoires, pour faire le service, pour chanter des cantiques et des actions de grâces aux portes de la résidence de l’Eternel.
Hezekiya kuma ya raba firistoci da Lawiyawa kashi-kashi, kowanne da hidimarsa, firistoci da Lawiyawa, don hadayu na ƙonawa da na salama, su yi hidima, su yi godiya, su kuma rera yabai a ƙofofin mazaunin Ubangiji.
3 Le roi fit don d’une part de ses biens pour les holocaustes, les holocaustes du matin et du soir, les holocaustes des sabbats, des néoménies et des fêtes, ainsi qu’il est écrit dans la loi de Moïse.
Sarki ya ba da taimako daga mallakarsa domin hadayun ƙonawa, safe da yamma da kuma don hadayun ƙonawa a Asabbatai, Sabon Wata da kuma ƙayyadaddun bukukkuwa kamar yadda yake a rubuce a cikin Dokar Ubangiji.
4 Il dit au peuple, aux habitants de Jérusalem, de donner la part des prêtres et des Lévites, afin qu’ils tinssent ferme à la loi de l’Eternel.
Ya umarci mutanen da suke zama a Urushalima su ba da rabon da yake na firistoci da Lawiyawa, don su ƙwallafa ransu ga Dokar Ubangiji.
5 Et quand la chose fut divulguée, les enfants d’Israël donnèrent en abondance les prémices du blé, du moût, de l’huile, du miel et de toutes les productions des champs et apportèrent en abondance la dîme de tout.
Nan da nan aka baza umarnin, sai Isra’ilawa suka bayar’ya’yan farin hatsinsu, sabon ruwan inabi, mai da kuma zuma da dukan abin da gona ta bayar, hannu sake. Suka kawo zakan kowane abu da yawa.
6 Les enfants d’Israël et de Juda qui demeuraient dans les villes de Juda, eux aussi, apportèrent la dîme du gros et du menu bétail, la dîme des choses saintes consacrées à l’Eternel, leur Dieu, et ils les donnèrent par monceaux.
Mutanen Isra’ila da Yahuda waɗanda suke zama a garuruwan Yahuda, su ma suka kawo zakan shanu da na tumaki da kuma zakan abubuwa masu tsarki da aka keɓe ga Ubangiji Allahnsu, suka jibge su tsibi-tsibi.
7 C’Est au troisième mois qu’ils commencèrent à former les monceaux, et au septième mois qu’ils les finirent.
Sun fara yin haka a wata na uku, suka kuma gama a wata na bakwai.
8 Ezéchias et les chefs arrivèrent, virent les monceaux et bénirent l’Eternel et son peuple Israël.
Sa’ad da Hezekiya da fadawansa suka zo suka ga tsibin, sai suka yabi Ubangiji, suka kuma albarkace mutanensa Isra’ila.
9 Ezéchias interrogea les prêtres et les Lévites au sujet de ces monceaux.
Hezekiya ya tambayi firistoci da Lawiyawa game da tsibin;
10 Alors Azariahou, le prêtre en chef de la maison de Çadok, lui répondit et dit: "Depuis qu’on a commencé d’apporter l’offrande au temple du Seigneur, on a mangé jusqu’à satiété et il en est resté énormément, car l’Eternel a béni son peuple, et c’est le reste que cette quantité que voici."
sai Azariya babban firist, daga iyalin Zadok ya amsa, “Tun daga lokacin da mutane suka fara kawo taimakonsu ga haikalin Ubangiji, muna da isashe don abinci da kuma da yawa da za mu rage, domin Ubangiji ya albarkaci mutanensa, saboda haka abin da ya ragu a rumbu yana da yawa.”
11 Ezéchias ordonna de préparer des chambres dans le temple de l’Eternel, et on les prépara.
Hezekiya ya ba da umarni a shirya ɗakunan ajiya a haikalin Ubangiji, aka kuwa yi haka.
12 On apporta fidèlement l’offrande, la dîme et les objets sacrés, que l’on confia à la surveillance de Conaniahou, le Lévite, et de Chimeï son frère, comme second.
Sa’an nan cikin aminci suka kawo taimako, zakka da keɓaɓɓun kyautai. Konaniya, wani Balawe, shi ne ke lura da waɗannan abubuwa, kuma ɗan’uwansa Shimeyi shi ne na biye da shi.
13 Yehiël, Azaziahou, Nahat, Assahel, Yerimôt, Yozabad, Eliël, Yismakhiahou, Mahat et Benayahou étaient préposés sous la direction de Conaniahou et de Chimeï, son frère, par ordre du roi Ezéchias et d’Azariahou, l’intendant du temple de Dieu.
Yehiyel, Azaziya, Nahat, Asahel, Yerimot, Yozabad, Eliyel, Ismakiya, Mahat da Benahiya su ne shugabanni, mataimakan Konaniya da Shimeyi ɗan’uwansa, waɗanda sarki Hezekiya da Azariya babban shugaban haikalin Allah suka naɗa.
14 Coré, fils de Yimna, le Lévite, gardien de la porte orientale, était préposé aux offrandes volontaires offertes à Dieu, pour donner l’offrande de l’Eternel et les choses éminemment saintes.
Kore ɗan Imna Balawe, mai tsaron Ƙofar Gabas, shi ne yake lura da baikon yardan ran da aka yi wa Allah, don ya karkasa bayarwar da aka keɓe domin Ubangiji da hadayu mafi tsarki.
15 Sous ses ordres étaient Eden, Miniamin, Yèchoua, Chemayahou, Amariahou, Chekhaniahou, dans les villes des prêtres pour donner loyalement les portions à leurs frères, suivant leurs divisions, aux grands comme aux petits.
Eden, Miniyamin, Yeshuwa, Shemahiya, Amariya da Shekaniya sun taimake shi da aminci a cikin garuruwan firistoci, suna ba da rabo wa’yan’uwansu firistoci bisa ga sassansu, tsofaffi da yara.
16 Outre ceux qui étaient inscrits comme mâles depuis trois ans et au-dessus, à tous ceux qui entraient dans le temple de l’Eternel, pour les fonctions quotidiennes, pour leur service, selon leurs classes et selon leurs divisions.
Bugu da ƙari, suka ba da rabo ga maza’yan shekaru uku ko fiye waɗanda sunayensu suna a tarihin zuriya, dukan waɗanda ba za su iya shiga haikalin Ubangiji su yi ayyukansu na kullum ba, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
17 L’Inscription des prêtres se faisait d’après leurs familles, et les Lévites étaient comptés depuis vingt ans et au-delà d’après leurs fonctions et leurs classes.
Suka kuma ba da rabo ga firistocin da aka rubuta ta iyalansu cikin tarihin zuriya, haka kuma ga Lawiyawa masu shekara ashirin ko fiye, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
18 Ils devaient enregistrer aussi leurs petits enfants, femmes, fils et filles avec toute l’assemblée, car ils s’occupaient ponctuellement de la distribution des choses saintes.
Suka haɗa da dukan ƙanana’ya’yansu, mata, da kuma’ya’ya maza da’ya’ya mata, al’umma gaba ɗaya da aka jera a waɗannan tarihin zuriya. Gama sun yi aminci cikin tsarkake kansu.
19 En outre, les descendants d’Aaron, les prêtres qui étaient à la campagne formant la banlieue de leurs villes avaient dans chaque ville des hommes désignés nominativement pour distribuer les portions à tous les mâles d’entre les prêtres et à tous ceux qui étaient enregistrés parmi les Lévites.
Akwai mutane a garuruwa da yawa waɗanda aka sa don su rarraba wa’ya’yan Haruna, firist, maza, waɗanda suke zaune a gonaki na ƙasar garuruwansu su ba kowane namijin da aka rubuta na Lawiyawa, rabonsa.
20 Ezéchias en fit autant dans tout Juda et il fit ce qui est bien, droit et loyal devant l’Eternel, son Dieu.
Abin da Hezekiya ya yi ke nan ko’ina a Yahuda, yana yin abin da yake da kyau, daidai da kuma mai aminci a gaban Ubangiji Allahnsa.
21 Dans toutes les œuvres qu’il entreprit pour le culte du temple de Dieu, pour la Loi et les commandements, recherchant son Dieu, il agit de tout cœur et réussit.
Cikin kome da ya yi cikin hidimar haikalin Allah, cikin biyayya kuma ga doka da umarnai, ya nemi Allahnsa, ya kuma yi aiki gabagadi. Ta haka kuwa ya yi nasara.

< 2 Chroniques 31 >