< 2 Chroniques 23 >

1 La septième année, Joïada prit courage et s’attacha par un pacte les centeniers Azaria, fils de Yeroham, Ismaël, fils de Johanan, Azariahou, fils d’Obed, Maassêyahou, fils d’Adaïahou, et Elichafat, fils de Zikhri.
A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
2 Ceux-ci parcoururent Juda en tout sens et rassemblèrent, de toutes les villes de Juda, les Lévites et les chefs de famille d’Israël, qui se rendirent à Jérusalem.
Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
3 Toute cette assemblée conclut un accord avec le roi dans la maison de Dieu, et Joïada leur dit: "Voici le fils du roi; il doit régner, selon la promesse faite par l’Eternel au sujet des descendants de David.
dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
4 C’Est ainsi que vous procéderez: un tiers d’entre vous, de ceux qui prennent la semaine en qualité de prêtres et de Lévites, gardera les entrées,
Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
5 un tiers surveillera la maison du roi, et un tiers, la porte de Yessod; et tout le peuple restera dans les cours de la maison de l’Eternel.
kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
6 Ainsi n’entreront dans le temple de l’Eternel que les prêtres et ceux qui font le service en qualité de Lévites; eux, ils peuvent entrer, car ils sont consacrés; quant au peuple tout entier, il doit respecter l’ordonnance de l’Eternel.
Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
7 Les Lévites feront cercle autour du roi, les armes à la main; quiconque voudra pénétrer dans le temple sera mis à mort. Vous accompagnerez le roi dans toutes ses démarches."
Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
8 Les Lévites et tout Juda exécutèrent fidèlement les ordres donnés par Joïada, le prêtre; ils prirent chacun leurs hommes, ceux qui commençaient et ceux qui avaient fini la semaine, car Joïada, le prêtre, n’avait pas congédié les sections.
Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
9 Le prêtre Joïada délivra aux centeniers les lances, les boucliers et autres armes ayant appartenu au roi David et déposées dans le temple de Dieu,
Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
10 et il rangea tout le peuple, armes en main, en partant du côté droit jusqu’au côté gauche du temple, de façon à entourer le roi.
Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
11 Puis, on fit sortir le fils du roi, on lui remit la couronne et le "témoignage"; on le proclama roi, Joïada et ses fils l’oignirent, et l’on cria "Vive le roi!"
Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
12 Athalie, entendant les cris du peuple qui accourait et acclamait le roi, se rendit au milieu de la foule dans le temple de l’Eternel.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
13 Elle regarda et vit ce spectacle: le roi debout sur son estrade à l’entrée, les chefs et les trompettes acclamant le roi, toute la foule manifestant sa joie en sonnant de la trompette, et les chanteurs, qui s’accompagnaient d’instruments de musique, donnant le signal des applaudissements. A cette vue, Athalie déchira ses vêtements et s’écria: "Trahison, trahison!"
Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
14 Le prêtre Joïada fit avancer les centeniers qui commandaient les troupes et leur dit: "Faites-la sortir des rangs, et qui la suivra, qu’on l’exécute avec le glaive!" Car le pontife avait recommandé qu’elle ne fût pas mise à mort dans la maison de l’Eternel.
Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
15 On fit place devant elle, et elle prit le chemin de l’entrée des chevaux pour se rendre au palais royal; là, on la mit à mort.
Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
16 Joïada conclut un pacte l’engageant lui, tout le peuple et le roi, à devenir le peuple de l’Eternel.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
17 Toute la foule pénétra dans le temple de Baal et le saccagea; on brisa ses autels et ses statues, on tua devant les autels Matân, prêtre de Baal.
Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
18 Le pontife plaça des surveillants dans la maison de l’Eternel, sous la direction des prêtres et des Lévites que David avait répartis en sections dans le temple du Seigneur, avec mission d’offrir les holocaustes à l’Eternel, conformément aux prescriptions de la Loi de Moïse, avec des manifestations de joie et des chants, selon le mode établi par David.
Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
19 Il disposa aussi les portiers près des portes du temple de l’Eternel pour en interdire l’accès à toute personne devenue impure par une cause quelconque.
Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
20 Il se fit accompagner par les centeniers, les notables, les principaux chefs du peuple et toute la population et conduisit le roi hors de la maison de l’Eternel; on entra dans le palais du roi, en franchissant la porte Supérieure, et on fit asseoir le roi sur le trône de la royauté.
Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
21 Tous les habitants du pays furent heureux, et la ville retrouva le calme. Quant à Athalie, on l’avait fait mourir par le glaive.
sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.

< 2 Chroniques 23 >