< 2 Chroniques 12 >

1 Une fois que Roboam eut affermi sa royauté et fut devenu puissant, il abandonna la Loi de l’Eternel, suivi de tout Israël.
Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
2 Dans la cinquième année du règne de Roboam, Sésak, roi d’Egypte, vint attaquer Jérusalem, parce qu’on était devenu infidèle au Seigneur;
Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
3 il disposait de douze cents chars, de soixante mille cavaliers. Innombrable était la multitude venue avec lui d’Egypte et composée de Libyens, de Soukkiites et d’Ethiopiens.
Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
4 Il s’empara des villes fortes de Juda et arriva jusqu’à Jérusalem.
ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
5 Alors Chemaya, le prophète, vint trouver Roboam et les grands de Juda qui s’étaient retirés à Jérusalem à l’approche de Sésak, et leur dit: "Ainsi parle le Seigneur: Vous m’avez abandonné, à mon tour je vous abandonne à la merci de Sésak."
Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
6 Les grands d’Israël et Roboam s’humilièrent et dirent: "L’Eternel est juste!"
Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
7 Le Seigneur, voyant qu’ils s’humiliaient, s’adressa à Chemaya en ces termes: "Ils se sont humiliés, je ne les détruirai point; mais encore un peu, j’assurerai leur salut, et mon courroux ne fondra pas sur Jérusalem par l’entremise de Sésak.
Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
8 Mais quand ils lui seront asservis, ils sauront ce que c’est de me servir ou de servir les royaumes étrangers."
Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
9 Sésak, roi d’Egypte, marcha donc contre Jérusalem: il s’empara des trésors de la maison du Seigneur et de ceux de la maison du roi, et emporta le tout. Il enleva aussi les boucliers d’or qu’avait fait faire Salomon.
Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
10 Le roi Roboam les remplaça par des boucliers de cuivre, dont il confia la garde aux chefs des coureurs chargés de surveiller l’entrée du palais royal.
Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
11 Chaque fois que le roi se rendait à la maison du Seigneur, les coureurs venaient porter les boucliers, puis les replaçaient dans leur salle de service.
Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
12 Comme il s’était humilié, la colère de l’Eternel se détourna de lui et n’acheva point sa ruine. Aussi bien, Juda avait conservé de bonnes qualités.
Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
13 Le roi Roboam s’affermit dans Jérusalem et continua de régner. En effet, Roboam était âgé de quarante et un ans à son avènement et il régna dix-sept ans à Jérusalem, la ville que le Seigneur avait choisie entre toutes les tribus d’Israël pour y faire dominer son nom. Sa mère se nommait Naama; elle était Ammonite.
Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
14 Il fit le mal, car il n’avait pas appliqué son cœur à rechercher l’Eternel.
Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
15 L’Histoire de Roboam, du début à la fin, se trouve consignée dans le récit du prophète Schemaya et du Voyant Iddo, avec les livres de généalogie. La guerre fut permanente entre Roboam et Jéroboam.
Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
16 Roboam s’endormit avec ses pères et fut enseveli dans la Cité de David. Il eut pour successeur son fils Abiyya.
Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chroniques 12 >