< 1 Samuel 2 >

1 Et Hanna se mit en prière, et elle dit: Mon cœur se délecte en l’Eternel, mon front s’est relevé grâce au Seigneur; je puis ouvrir la bouche en face de mes ennemis, car j’ai à me réjouir, Seigneur, de ton assistance.
Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
2 Nul n’est saint comme l’Eternel, nul ne l’est que toi seul! Aucune Puissance n’égale notre Dieu.
“Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
3 Cessez, cessez vos paroles arrogantes, les bravades qui s’exhalent de votre bouche; car il dispose de toute science, l’Eternel, et toute œuvre lui est facile.
“Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
4 Par lui, l’arc des forts est brisé, et ceux qui faiblissent sont armés de vigueur;
“An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
5 Ceux qui vivaient dans l’abondance se font mercenaires, et qui souffrait de la faim en est délivré; tandis que la femme stérile enfante sept fois, la mère féconde est humiliée.
Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
6 L’Eternel fait mourir et fait vivre; il précipite au tombeau, et en retire. (Sheol h7585)
“Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
7 L’Eternel appauvrit et enrichit, abaisse et relève à son gré.
Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
8 Il redresse l’humble couché dans la poussière, fait remonter le pauvre du sein de l’abjection, pour les placer à côté des grands et les installer sur un siège d’honneur; car les colonnes de la terre sont à l’Eternel, c’est lui qui en a fait les supports du monde.
Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
9 Il veille sur les pas de ses adorateurs, tandis que les impies périssent dans les ténèbres, car ce n’est pas la force qui fait le vainqueur.
Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
10 L’Eternel, ses agresseurs sont foudroyés, quand sur eux, du haut du ciel, Il tonne; l’Eternel juge les sommités de la terre! Et Il donnera la puissance à son roi, et Il exaltera la gloire de son élu.
waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
11 Elkana s’en retourna chez lui à Rama, et le jeune homme resta pour servir le Seigneur, sous les yeux du pontife Héli.
Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
12 Or, les fils d’Héli étaient des hommes pervers qui ne s’inquiétaient pas du Seigneur.
’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
13 Voici comme ces prêtres en usaient avec le peuple: chaque fois qu’un individu offrait un sacrifice, le serviteur du prêtre survenait pendant la cuisson de la viande, ayant en main la fourchette à trois dents,
Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
14 qu’il piquait dans la marmite, la chaudière, la casserole ou le pot; et tout ce qu’amenait la fourchette, le prêtre se l’appropriait. Telle était leur pratique envers tout Israélite qui venait sacrifier à Silo.
zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
15 Bien mieux: avant qu’on fît fumer la graisse des victimes, le serviteur du prêtre venait dire à l’offrant: "Donne de la viande à rôtir pour le prêtre, car il n’accepte de toi que de la viande crue et non cuite."
Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
16 Que si l’homme disait: "On doit d’abord faire fumer les parties grasses, tu prendras après ce qu’il te plaira", on lui répondait: "Non, donne tout de suite, sinon je prendrai de force!"
In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
17 Le péché de ces jeunes gens était très grave aux yeux de l’Eternel, en ce qu’ils avilissaient le culte du Seigneur.
Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
18 Pour le jeune Samuel, il faisait le service devant le Seigneur, vêtu d’un éphod de lin,
Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
19 outre un petit manteau que sa mère lui faisait et lui apportait tous les ans, lorsqu’elle venait là avec son mari pour le sacrifice annuel.
Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
20 Et Héli bénissait Elkana et sa femme en disant: "Que l’Eternel t’accorde par cette femme une nouvelle postérité, en échange de l’enfant qui a été voué au Seigneur!" et ils s’en retournaient à la maison.
Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
21 De fait, le Seigneur se souvint de Hanna, laquelle conçut et enfanta trois fils et deux filles, tandis que le jeune Samuel grandissait en présence du Seigneur.
Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
22 Or, Héli était très vieux, et il entendait parler de la conduite de ses fils envers tout Israël, et comme quoi ils abusaient des femmes qui venaient faire leurs dévotions à l’entrée de la tente d’assignation.
To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
23 Et il leur dit: "Pourquoi faites-vous de pareilles choses? Car j’entends les fâcheux propos dont vous êtes l’objet de la part de tout ce peuple.
Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
24 Cessez donc, mes enfants; car il n’est pas beau, le bruit que j’entends courir sur vous parmi le peuple du Seigneur.
A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
25 Si un homme offense un autre homme, le juge en fait justice; mais si c’est Dieu lui-même qu’il offense, qui intercédera pour lui?…" Mais ils n’écoutaient point leur père; aussi Dieu résolut de les faire mourir.
In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
26 Cependant le jeune Samuel grandissait et gagnait de plus en plus la faveur de Dieu et celle des hommes.
Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
27 Un homme de Dieu vint trouver Héli et lui dit: "Ainsi parle l’Eternel: Quoi! Je me suis manifesté à tes pères, alors qu’ils étaient en Egypte, soumis à la maison de Pharaon,
Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
28 et je les ai choisis entre toutes les tribus d’Israël pour être mes pontifes, pour monter sur mon autel, pour m’offrir l’encens et porter l’éphod devant moi, et j’ai donné à ta famille une part de tous les sacrifices des enfants d’Israël;
Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
29 et maintenant vous foulez aux pieds mes sacrifices et mes offrandes, que j’avais ordonnés pour le sanctuaire! Et tu honores tes fils plus que moi! Et vous vous engraissez du meilleur des offrandes d’Israël, des dons de mon peuple!
Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
30 Eh bien! Ainsi parle l’Eternel, Dieu d’Israël: J’Avais décidé que ta famille et celle de ton père fonctionneraient devant moi à perpétuité; et maintenant, dit le Seigneur, loin de moi cette pensée! Car j’honore qui m’honore, et qui m’outrage sera livré au mépris.
“Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
31 Oui, un temps viendra où je couperai court à ta force et à celle de ta famille, de manière que nul n’y vieillira.
Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
32 Tu connaîtras les angoisses domestiques au milieu des prospérités d’Israël, et jamais, dans ta famille, on n’atteindra à la vieillesse.
Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
33 Je ne retrancherai pas tous les tiens du service de mon autel, et cela pour que tes yeux se consument et que ton âme se désole, en voyant tout espoir de ta race s’éteindre à l’âge d’homme.
Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
34 Je t’en donne pour présage ce qui arrivera à tes deux fils, Hophni et Phinéas: tous deux mourront le même jour.
“‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
35 Et je m’instituerai un prêtre fidèle, qui se conduira selon mon cœur et dans mon esprit; et je lui édifierai une maison durable, qui fonctionnera devant mon oint constamment.
Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
36 Et ceux qui resteront alors de ta famille viendront se jeter à ses pieds pour une pièce d’argent, pour un morceau de pain, en disant: De grâce, admets-moi à quelque service sacerdotal, pour que j’aie du pain à manger!"
Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”

< 1 Samuel 2 >