< Romains 11 >

1 Je dis donc: Dieu a-t-il rejeté son peuple? Qu’ainsi n’advienne! Car moi aussi je suis Israélite, de la semence d’Abraham, de la tribu de Benjamin.
Sai na ce, Allah ya ki mutanensa ne? Ba zai taba yiwuwa ba. Domin ni ma ba-Isra'ile ne, na zuriyar Ibrahim, a kabilar Bilyaminu.
2 Dieu n’a point rejeté son peuple, lequel il a préconnu. Ne savez-vous pas ce que l’écriture dit dans [l’histoire d’]Élie, comment il fait requête à Dieu contre Israël?
Allah bai ki mutanen sa da ya ke da rigyasaninsu ba. Ko kun san abin da nassi ya ce game da Iliya, yadda ya kai karar Isra'ila a gaban Allah?
3 « Seigneur, ils ont tué tes prophètes; ils ont renversé tes autels; et moi, je suis demeuré seul, et ils cherchent ma vie. »
Ya ce, ''Ubangiji, sun kashe annabawanka, sun rushe alfarwanka kuma, Ni kadai ne na rage, ga shi suna neman su kashe ni.''
4 Mais que lui dit la réponse divine? « Je me suis réservé 7 000 hommes qui n’ont pas fléchi le genou devant Baal ».
Amma wacce amsa ce Allah ya ba shi? Ya ce, ''Ina da mutane dubu bakwai da na kebe don kaina, da ba su taba rusuna wa Ba'al ba.''
5 Ainsi donc, au temps actuel aussi, il y a un résidu selon [l’]élection de [la] grâce.
Ban da haka ma, ban da haka ma a wannan lokacin akwai sauran zabe na alheri.
6 Or, si c’est par la grâce, ce n’est plus sur le principe des œuvres, puisque autrement la grâce n’est plus [la] grâce.
Amma tun da ta wurin alheri ne, ba ga ayyuka ba. In ba haka ba, alheri ba zai zama alheri ba kenan.
7 Quoi donc? Ce qu’Israël recherche, il ne l’a pas obtenu, mais l’élection l’a obtenu, et les autres ont été endurcis,
Sai kuma me? Abin da Isra'ila ke nema, ba su samu ba, amma zababbun sun same shi, saura kuma sun taurare.
8 selon qu’il est écrit: « Dieu leur a donné un esprit d’étourdissement, des yeux pour ne point voir et des oreilles pour ne point entendre, jusqu’au jour d’aujourd’hui ».
Kamar yadda yake a rubuce, ''Allah ya ba su ruhun rashin fahimta, ga idanu amma ba za su gani ba, ga kunnuwa amma ba za su ji ba, har zuwa wannan rana.''
9 Et David dit: « Que leur table devienne pour eux un filet, et un piège, et une occasion de chute, et une rétribution;
Dauda kuma ya ce, ''bari teburinsu ya zama taru, da tarko, ya zama dutsen tuntube da abin ramako a gare su.
10 que leurs yeux soient obscurcis pour ne point voir; et courbe continuellement leur dos ».
Bari idanunsu ya duhunta domin kada su gani; bayansu kuma a duke kullum.''
11 Je dis donc: Ont-ils bronché afin qu’ils tombent? Qu’ainsi n’advienne! Mais par leur chute, le salut [parvient] aux nations pour les exciter à la jalousie.
Na ce, ''sun yi tuntube domin su fadi ne?'' Kada abu kamar haka ya faru. A maimakon haka, juyawa baya da suka yi ya sa, ceto ya zo ga Al'ummai, domin ya sa su kishi.
12 Or, si leur chute est la richesse du monde, et leur diminution, la richesse des nations, combien plus le sera leur plénitude!
Idan yanzu juyawa baya da sun yi ya zama arziki ga duniya, rashin su kuma arziki ga Al'ummai, yaya kwatancin girmansa zai kasance in sun zo ga kammala?
13 Car je parle à vous, nations, en tant que moi je suis en effet apôtre des nations, je glorifie mon ministère,
Yanzu ina magana da ku ku da ke Al'ummai. Tunda yake ni ne manzo ga Al'ummai, ina kuma fahariya cikin hidimata.
14 si en quelque façon je puis exciter à la jalousie ma chair et sauver quelques-uns d’entre eux.
Yana yiwuwa in sa ''yan'uwa na kishi, domin mu ceci wadansu su.
15 Car si leur mise à l’écart est la réconciliation du monde, quelle sera leur réception, sinon la vie d’entre les morts.
Idan kinsu ya kawo sulhuntawa ga duniya, Karbarsu kuma zata zama yaya? Zata zama rai ne daga mutuwa.
16 Or, si les prémices sont saintes, la masse l’est aussi; et si la racine est sainte, les branches le sont aussi.
'ya'yan farko sunan haka ma kakkabensu yake, Idan saiwar itace na nan, haka ma rassan za su zama.
17 Or, si quelques-unes des branches ont été arrachées, et si toi qui étais un olivier sauvage, as été enté au milieu d’elles, et es devenu coparticipant de la racine et de la graisse de l’olivier,
Amma idan an karye wasu daga cikin rassan, idan ku rassan zaitun na ainihi ne, da aka samu daga cinkinsu, kuma idan kuna da gado tare da su, acikin saiwar itacen zaitun din.
18 ne te glorifie pas contre les branches; mais si tu te glorifies, ce n’est pas toi qui portes la racine, mais c’est la racine qui te porte.
Kada ku yi fahariya a kan rassan. Amma idan kuka yi fahariya to ba ku bane masu karfafa saiwar amma saiwar ce ke karfafa ku.
19 Tu diras donc: Les branches ont été arrachées, afin que moi je sois enté.
Kana iya cewa, ''An karye rassan domin a same ni a ciki.''
20 Bien! elles ont été arrachées pour cause d’incrédulité, et toi tu es debout par la foi. Ne t’enorgueillis pas, mais crains
Wannan gaskiya ne! Saboda rashin bangaskiyarsu ne ya sa aka karye su daga rassan, amma ku tsaya da karfi acikin bangaskiyarku. Kada ku dauki kanku fiye da yadda ya kamata, amma ku ji tsoro.
21 (si en effet Dieu n’a pas épargné les branches [qui sont telles] selon la nature), qu’il ne t’épargne pas non plus.
Domin idan Allah bai bar ainihin rassan ba, to ba zai bar ku ba.
22 Considère donc la bonté et la sévérité de Dieu: la sévérité envers ceux qui sont tombés; la bonté de Dieu envers toi, si tu persévères dans cette bonté; puisque autrement, toi aussi, tu seras coupé.
Ku duba yadda irin ayyuka masu tsananni na Allah. Ta daya hannun kuma, tsanannin kan zoa kan Yahudawa wadanda suka fadi. Har 'ila yau jinkai Allah ya zo maku, idan kun cigaba cikin alherinsa baza a sare ku ba. Amma in kun ki za a sare ku.
23 Et eux aussi, s’ils ne persévèrent pas dans l’incrédulité, ils seront entés, car Dieu est puissant pour les enter de nouveau.
Hakanan, idan ba su ci gaba cikin rashin bangaskiyarsu ba, za a maida su cikin itacen. Domin Allah zai iya sake maida su.
24 Car si toi, tu as été coupé de l’olivier qui selon la nature était sauvage, et as été enté contre nature sur l’olivier franc, combien plus ceux qui en sont selon la nature seront-ils entés sur leur propre olivier?
Idan an yanke ka daga itacen zaitun da ke na jeji, har ya yiwu an hada ka cikin itacen zaitun na ainihi, yaya kuma wadannan Yahudawa wadanda sune ainihin rassan, da za'a maido cikin zaitun da ke na ainihi?
25 Car je ne veux pas, frères, que vous ignoriez ce mystère-ci, afin que vous ne soyez pas sages à vos propres yeux: c’est qu’un endurcissement partiel est arrivé à Israël jusqu’à ce que la plénitude des nations soit entrée;
Yan'uwa, ba na so ku kasance cikin duhu a game da wannan asirin, domin kada ku zama da hikima cikin tunaninku. Wannan asirin shine cewa wannan taurarewa ta faru a Isra'ila, har sai da Al'ummai suka shigo ciki.
26 et ainsi tout Israël sera sauvé, selon qu’il est écrit: « Le libérateur viendra de Sion; il détournera de Jacob l’impiété.
Ta haka dukan Isra'ila za su tsira, kamar yadda yake a rubuce: ''Daga cikin Sihiyona mai Kubutarwa zai fito; Zai kawar da kazanta daga cikin Yakubu.
27 Et c’est là l’alliance de ma part pour eux, lorsque j’ôterai leurs péchés ».
Wannan zai zama alkawarina da su, sa'adda na kawar da zunubansu.''
28 En ce qui concerne l’évangile, ils sont ennemis à cause de vous; mais en ce qui concerne l’élection, ils sont bien-aimés à cause des pères.
A wani bangaren kuma game da bishara, su makiya ne amamadinku, ta wani fannin kuma bisa ga zabin Allah su kaunattatu ne saboda ubanni.
29 Car les dons de grâce et l’appel de Dieu sont sans repentir.
Domin baye-baye da kiran Allah basa canzawa.
30 Car comme vous aussi vous avez été autrefois désobéissants à Dieu et que maintenant vous êtes devenus des objets de miséricorde par la désobéissance de ceux-ci,
Domin ku ma da ba ku yin biyayya ga Allah, amma yanzu kun sami jinkai saboda rashin biyayyarsu.
31 de même ceux-ci aussi ont été maintenant désobéissants à votre miséricorde, afin qu’eux aussi deviennent des objets de miséricorde.
Ta wannan hanyar dai, wadannan Yahudawan sun zama marasa biyayya. Sakamakon haka shine ta wurin jinkan da aka nuna maku, suma su samu jikai yanzu.
32 Car Dieu a renfermé tous, [Juifs et nations], dans la désobéissance, afin de faire miséricorde à tous. (eleēsē g1653)
Domin Allah ya rufe kowa ga rashin biyayya, domin ya nuna jinkai ga kowa. (eleēsē g1653)
33 Ô profondeur des richesses et de la sagesse et de la connaissance de Dieu! Que ses jugements sont insondables, et ses voies introuvables!
Ina misalin zurfin wadata da kuma hikima da sani na Allah! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban a bincika, hanyoyinsa kuma sun fi gaban ganewa!
34 Car qui a connu la pensée du Seigneur, ou qui a été son conseiller?
Don wanene ya san tunanin Ubangiji? Wanene kuma ya zama mai bashi shawara?
35 ou qui lui a donné le premier, et il lui sera rendu?
Ko kuma, wanene ya fara ba Allah wani abu, domin a biya shi?''
36 Car de lui, et par lui, et pour lui, sont toutes choses! À lui soit la gloire éternellement! Amen. (aiōn g165)
Daga wurinsa ne, ta wurinsa ne kuma, a gare shi ne kuma dukan abu suka fito. A gare shi daukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn g165)

< Romains 11 >