< Psaumes 94 >

1 Dieu des vengeances, Éternel, Dieu des vengeances! fais luire ta splendeur.
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Élève-toi, juge de la terre! rends la récompense aux orgueilleux.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 Jusques à quand les méchants, ô Éternel! jusques à quand les méchants se réjouiront-ils?
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 [Jusques à quand] tous les ouvriers d’iniquité proféreront-ils [et] diront-ils des paroles arrogantes? [jusques à quand] se vanteront-ils?
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 Ils foulent ton peuple, ô Éternel! et affligent ton héritage;
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 Ils tuent la veuve et l’étranger, et mettent à mort les orphelins,
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 Et ils disent: Jah ne le verra pas, et le Dieu de Jacob n’y fera pas attention.
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Comprenez, vous les stupides d’entre le peuple! Et vous, insensés, quand serez-vous intelligents?
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 Celui qui a planté l’oreille n’entendra-t-il point? Celui qui a formé l’œil ne verra-t-il point?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 Celui qui instruit les nations ne châtiera-t-il pas, lui qui enseigne la connaissance aux hommes?
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 L’Éternel connaît les pensées des hommes, qu’elles ne sont que vanité.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Bienheureux l’homme que tu châties, ô Jah! et que tu enseignes par ta loi,
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 Pour le mettre à l’abri des mauvais jours, jusqu’à ce que la fosse soit creusée pour le méchant!
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 Car l’Éternel ne délaissera point son peuple et n’abandonnera point son héritage;
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 Car le jugement retournera à la justice, et tous ceux qui sont droits de cœur le suivront.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Qui se lèvera pour moi contre les méchants? Qui se tiendra avec moi contre les ouvriers d’iniquité?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 Si l’Éternel n’avait été mon aide, peu s’en serait fallu que mon âme n’ait été habiter dans le silence.
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 Si j’ai dit: Mon pied glisse, ta bonté, ô Éternel! m’a soutenu.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 Dans la multitude des pensées qui étaient au-dedans de moi, tes consolations ont fait les délices de mon âme.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Le trône d’iniquité, qui fait de l’oppression une loi, sera-t-il uni à toi?
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 Ils se rassemblent contre l’âme du juste, et condamnent le sang innocent.
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 Mais l’Éternel me sera une haute retraite, et mon Dieu, le rocher de ma confiance.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 Il fera retomber sur eux leur iniquité, et les détruira par leur méchanceté; l’Éternel, notre Dieu, les détruira.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Psaumes 94 >