< Psaumes 9 >
1 Au chef de musique. Sur Muth-Labben. Psaume de David. Je célébrerai l’Éternel de tout mon cœur; je raconterai toutes tes merveilles.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ga muryar “Mutuwar Ɗa.” Zabura ta Dawuda. Zan yabe ka, ya Ubangiji, da dukan zuciyata; zan faɗa dukan abubuwan banmamakinka.
2 Je me réjouirai et je m’égaierai en toi; je chanterai ton nom, ô Très-haut!
Zan yi murna in kuma yi farin ciki a cikinka; zan rera yabo ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka.
3 Quand mes ennemis sont retournés en arrière, ils ont bronché, et ont péri devant toi.
Abokan gābana sun ja da baya; suka yi tuntuɓe suka hallaka a gabanka.
4 Car tu as maintenu mon droit et ma cause; tu t’es assis sur le trône, toi qui juges justement.
Gama ka tabbata da gaskiyata da kuma abin da nake yi; ka zauna a kujerarka, kana yin shari’a da adalci.
5 Tu as tancé les nations, tu as fait périr le méchant; tu as effacé leur nom pour toujours et à perpétuité.
Ka tsawata wa ƙasashe ka kuma hallakar da mugaye; ka shafe sunansu har abada abadin.
6 Ô ennemi! les dévastations sont venues à leur fin pour toujours. Tu as aussi rasé des villes, leur mémoire a péri avec elles.
Lalaci marar ƙarewa ya cimma abokan gābanmu, ka tuttumɓuke biranensu; yadda ma ba aka ƙara tunaninsu.
7 Mais l’Éternel est assis pour toujours; il a préparé son trône pour le jugement,
Ubangiji yana mulki har abada; ya kafa kujerarsa don shari’a.
8 Et il jugera le monde avec justice, et exercera le jugement sur les peuples avec droiture.
Zai hukunta duniya da adalci; zai yi mulkin mutane cikin gaskiya.
9 Et l’Éternel sera une haute retraite pour l’opprimé, une haute retraite dans les temps de détresse.
Ubangiji shi ne mafakan waɗanda ake danniya, mafaka a lokutan wahala.
10 Et ceux qui connaissent ton nom se confieront en toi; car tu n’as pas abandonné ceux qui te cherchent, ô Éternel!
Waɗanda suka san sunanka za su dogara da kai, gama kai, Ubangiji, ba ka taɓa yashe waɗanda suke nemanka ba.
11 Chantez à l’Éternel qui habite en Sion, annoncez parmi les peuples ses [hauts] faits.
Rera yabai ga Ubangiji, wanda yake zaune a kursiyi a Sihiyona; yi shela a cikin al’ummai abin da ya aikata.
12 Car en recherchant le sang il se souvient d’eux; il n’oublie pas le cri des affligés.
Gama shi da yakan ɗauki fansa a kan mai kisa yakan tuna; ba ya ƙyale kukan masu wahala.
13 Ô Éternel! use de grâce envers moi; regarde mon affliction [que je souffre] de la part de ceux qui me haïssent, toi qui me fais remonter des portes de la mort;
Ya Ubangiji, dubi yadda abokan gābana suna tsananta mini! Ka yi jinƙai ka kuma ɗaga ni daga ƙofofin mutuwa,
14 Afin que je raconte toutes tes louanges dans les portes de la fille de Sion. Je me réjouirai en ton salut.
don in furta yabanka cikin ƙofofin’Yar Sihiyona a can kuwa in yi farin ciki cikin cetonka.
15 Les nations se sont enfoncées dans la fosse qu’elles ont faite; au filet même qu’elles ont caché, leur pied a été pris.
Al’umma sun fāɗa cikin ramin da suka haƙa wa waɗansu; aka kama ƙafafunsu a ragar da suka ɓoye.
16 L’Éternel s’est fait connaître par le jugement qu’il a exécuté; le méchant est enlacé dans l’œuvre de ses mains. Higgaïon. (Sélah)
An san Ubangiji ta wurin gaskiyarsa; an kama mugaye da aikin hannuwansu. Haggayiyon. (Sela)
17 Les méchants seront repoussés jusque dans le shéol, toutes les nations qui oublient Dieu; (Sheol )
Mugaye za su koma kabari, dukan al’umman da suka manta da Allah. (Sheol )
18 Car le pauvre ne sera pas oublié à jamais, l’attente des débonnaires ne périra pas pour toujours.
Amma har abada ba za a manta da mai bukata ba, ba kuwa sa zuciyar mai wahala zai taɓa hallaka.
19 Lève-toi, Éternel! que l’homme ne prévale pas. Que les nations soient jugées devant ta face.
Ka tashi, ya Ubangiji, kada ka bar wani yă yi nasara; bari a hukunta al’ummai a gabanka.
20 Éternel! remplis-les de frayeur. Que les nations sachent qu’elles ne sont que des hommes. (Sélah)
Ka buge su da rawar jiki, ya Ubangiji; bari al’ummai su sani su mutane ne kurum. (Sela)