< Psaumes 87 >
1 Des fils de Coré. Psaume. Cantique. La fondation qu’il a posée est dans les montagnes de sainteté.
Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Waƙa ce. Ya kafa harsashinsa a kan dutse mai tsarki.
2 L’Éternel aime les portes de Sion plus que toutes les demeures de Jacob.
Ubangiji yana ƙaunar ƙofofin Sihiyona fiye da dukan wuraren zaman Yaƙub.
3 Des choses glorieuses sont dites de toi, cité de Dieu. (Sélah)
Ana faɗin abubuwa masu ɗaukaka game da ke Ya birnin Allah, (Sela)
4 Je ferai mention de Rahab et de Babylone à ceux qui me connaissent; voici la Philistie, et Tyr, avec l’Éthiopie: celui-ci était né là.
“Zan lissafta Rahab a cikin waɗanda suka san ni, Filistiya ita ma, da Taya, tare da Kush, zan kuma ce, ‘An haifi wannan a Sihiyona.’”
5 Et de Sion il sera dit: Celui-ci et celui-là sont nés en elle; et le Très-haut, lui, l’établira.
Tabbatacce, game da Sihiyona za a ce, “Wannan da wancan an haifa a cikinta, Mafi Ɗaukaka kansa zai kafa ta.”
6 Quand l’Éternel enregistrera les peuples, il comptera: Celui-ci est né là. (Sélah)
Ubangiji zai rubuta a littafin sunayen mutanensa, “An haifi wannan a Sihiyona.” (Sela)
7 Et en chantant et en dansant, [ils diront]: Toutes mes sources sont en toi!
Yayinda suke kaɗe-kaɗe za su rera, “Dukan maɓulɓulaina suna cikinki.”