< Psaumes 83 >
1 Cantique. Psaume d’Asaph. Ô Dieu! ne garde pas le silence. Ne te tais pas, et ne te tiens pas tranquille, ô Dieu!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Car voici, tes ennemis s’agitent, et ceux qui te haïssent lèvent la tête.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Ils trament avec astuce des complots contre ton peuple, et ils consultent contre tes [fidèles] cachés.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Ils ont dit: Venez, et exterminons-les, de sorte qu’ils ne soient plus une nation et qu’on ne fasse plus mention du nom d’Israël.
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Car ils ont consulté ensemble d’un cœur, ils ont fait une alliance contre toi:
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 Les tentes d’Édom, et les Ismaélites, Moab, et les Hagaréniens,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Guebal, et Ammon, et Amalek, la Philistie, avec les habitants de Tyr;
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Assur aussi s’est joint à eux; ils servent de bras aux fils de Lot. (Sélah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Fais-leur comme à Madian, – comme à Sisera, comme à Jabin au torrent de Kison,
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Qui ont été détruits à En-Dor, qui sont devenus du fumier pour la terre.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Fais que leurs nobles soient comme Oreb et comme Zeëb, et tous leurs princes comme Zébakh et comme Tsalmunna;
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Car ils ont dit: Prenons possession des habitations de Dieu.
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Mon Dieu! rends-les semblables à un tourbillon, comme la balle devant le vent.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Comme le feu brûle la forêt, et comme la flamme embrase les montagnes,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 Ainsi poursuis-les par ta tempête, et épouvante-les par ton ouragan.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Remplis leurs faces d’ignominie, afin qu’ils cherchent ton nom, ô Éternel!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Qu’ils soient honteux et épouvantés à jamais, qu’ils soient confondus et qu’ils périssent;
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Et qu’ils sachent que toi seul, dont le nom est l’Éternel, tu es le Très-haut sur toute la terre.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.