< Psaumes 71 >

1 En toi, Éternel! j’ai mis ma confiance: que je ne sois jamais confus!
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 Dans ta justice, délivre-moi et fais que j’échappe; incline ton oreille vers moi et sauve-moi.
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 Sois pour moi un rocher d’habitation, afin que j’y entre continuellement; tu as donné commandement de me sauver, car tu es mon rocher et mon lieu fort.
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Mon Dieu! fais-moi échapper de la main du méchant, de la main de l’injuste et de l’oppresseur.
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 Car toi tu es mon attente, Seigneur Éternel! ma confiance dès ma jeunesse.
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 Je me suis appuyé sur toi dès le ventre; c’est toi qui m’as tiré hors des entrailles de ma mère: tu es le sujet continuel de ma louange.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 Je suis pour plusieurs comme un prodige; mais toi, tu es mon fort refuge.
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 Ma bouche est pleine de ta louange [et] de ta magnificence, tout le jour.
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Ne me rejette pas au temps de [ma] vieillesse; ne m’abandonne pas quand ma force est consumée.
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 Car mes ennemis parlent contre moi, et ceux qui guettent mon âme consultent ensemble,
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 Disant: Dieu l’a abandonné; poursuivez-le et saisissez-le, car il n’y a personne qui le délivre.
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 Ô Dieu! ne te tiens pas loin de moi; mon Dieu, hâte-toi de me secourir!
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 Qu’ils soient honteux, qu’ils soient consumés, ceux qui sont ennemis de mon âme; qu’ils soient couverts d’opprobre et de confusion, ceux qui cherchent mon malheur.
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 Mais moi, j’attendrai continuellement, et je redirai sans cesse toutes tes louanges.
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 Ma bouche racontera tout le jour ta justice [et] ton salut, car je n’en connais pas l’énumération.
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 J’irai dans la puissance du Seigneur Éternel; je ferai mention de ta justice, de la tienne seule.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 Ô Dieu! tu m’as enseigné dès ma jeunesse; et jusqu’ici j’ai annoncé tes merveilles.
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 Et aussi, jusqu’à la vieillesse et aux cheveux blancs, ô Dieu! ne m’abandonne pas, jusqu’à ce que j’annonce ton bras à [cette] génération, ta puissance à tous ceux qui viendront.
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 Et ta justice, ô Dieu! est haut élevée. Toi qui as fait de grandes choses, ô Dieu! qui est comme toi?
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 Toi qui nous as fait voir de nombreuses et amères détresses, tu nous redonneras la vie, et tu nous feras remonter hors des profondeurs de la terre.
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 Tu multiplieras ma grandeur, et tu te tourneras, tu me consoleras.
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 Aussi, mon Dieu, je te célébrerai avec le luth, [je louerai] ta vérité; je chanterai tes louanges avec la harpe, ô Saint d’Israël!
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 Mes lèvres, et mon âme, que tu as rachetée, exulteront quand je chanterai tes louanges.
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 Ma langue aussi redira tout le jour ta justice; car ils seront honteux, car ils seront confondus, ceux qui cherchent mon malheur.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< Psaumes 71 >