< Psaumes 66 >

1 Au chef de musique. Cantique. Psaume. Poussez des cris de joie vers Dieu, toute la terre!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Chantez la gloire de son nom, rendez glorieuse sa louange.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Dites à Dieu: Que tes œuvres sont terribles! Tes ennemis se soumettent à toi, à cause de la grandeur de ta force.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Toute la terre se prosternera devant toi, et chantera tes louanges; elle chantera ton nom. (Sélah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Venez, et voyez les œuvres de Dieu: il est terrible dans ses actes envers les fils des hommes.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Il changea la mer en terre sèche; ils passèrent le fleuve à pied: là nous nous sommes réjouis en lui.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Il domine par sa puissance pour toujours; ses yeux observent les nations. Que les rebelles ne s’élèvent pas! (Sélah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Peuples, bénissez notre Dieu, et faites entendre la voix de sa louange.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 C’est lui qui a conservé notre âme en vie, et il n’a pas permis que nos pieds soient ébranlés.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Car, ô Dieu! tu nous as éprouvés, tu nous as affinés comme on affine l’argent;
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Tu nous as fait entrer dans le filet, tu as mis un fardeau accablant sur nos reins;
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Tu as fait passer les hommes sur notre tête; nous sommes entrés dans le feu et dans l’eau, et tu nous as fait sortir dans un lieu spacieux.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 J’entrerai dans ta maison avec des holocaustes; j’acquitterai envers toi mes vœux,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Ce que mes lèvres ont proféré, et que ma bouche a dit dans ma détresse.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Je t’offrirai des holocaustes de bêtes grasses, avec l’encens des béliers; je sacrifierai du gros bétail avec des boucs. (Sélah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Venez, écoutez, vous tous qui craignez Dieu, et je raconterai ce qu’il a fait pour mon âme.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 J’ai crié à lui de ma bouche, et il a été exalté par ma langue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Si j’avais regardé l’iniquité dans mon cœur, le Seigneur ne m’aurait pas écouté.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Cependant Dieu m’a écouté; il a fait attention à la voix de ma prière.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Béni soit Dieu, qui n’a point rejeté ma prière, ni retiré d’avec moi sa bonté.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psaumes 66 >