< Psaumes 63 >

1 Psaume de David; quand il était dans le désert de Juda. Ô Dieu! tu es mon Dieu; je te cherche au point du jour; mon âme a soif de toi, ma chair languit après toi, dans une terre aride et altérée, sans eau,
Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
2 Pour voir ta force et ta gloire, comme je t’ai contemplé dans le lieu saint.
Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
3 Car ta bonté est meilleure que la vie; mes lèvres te loueront.
Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
4 Ainsi je te bénirai durant ma vie, j’élèverai mes mains en ton nom.
Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
5 Mon âme est rassasiée comme de moelle et de graisse, et ma bouche [te] louera avec des lèvres qui chantent de joie.
Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
6 Quand je me souviens de toi sur mon lit, je médite de toi durant les veilles de la nuit;
A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
7 Car tu as été mon secours, et à l’ombre de tes ailes je chanterai de joie.
Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
8 Mon âme s’attache à toi pour te suivre, ta droite me soutient.
Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
9 Mais ceux qui cherchent ma vie pour sa ruine entreront dans les parties inférieures de la terre;
Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
10 On les livrera à la puissance de l’épée, ils seront la portion des renards.
Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
11 Mais le roi se réjouira en Dieu, [et] quiconque jure par lui se glorifiera; car la bouche de ceux qui parlent faussement sera fermée.
Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.

< Psaumes 63 >