< Psaumes 62 >

1 Au chef de musique. Sur Jeduthun. Psaume de David. Sur Dieu seul mon âme se repose paisiblement; de lui vient mon salut.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Zaburar Dawuda. Raina na samun hutu a wurin Allah ne kaɗai; cetona na zuwa daga gare shi.
2 Lui seul est mon rocher et mon salut, ma haute retraite; je ne serai pas beaucoup ébranlé.
Shi kaɗai ne dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
3 Jusques à quand vous jetterez-vous sur un homme, [et chercherez]-vous tous à le renverser comme une muraille qui penche, comme un mur qui va crouler?
Har yaushe za ku tasar wa mutum guda? Dukanku ne za ku kā da shi wannan jinganannen bango, wannan rusasshen katanga?
4 Ils ne consultent que pour [le] précipiter de son élévation; ils prennent plaisir au mensonge; ils bénissent de leur bouche, et intérieurement ils maudissent. (Sélah)
Sun kintsa sosai su tumɓuke shi daga matsayinsa mai martaba; suna jin daɗi yin ƙarairayi. Sukan sa wa mutum albarka da bakinsu, amma a zuciyarsu la’antawa suke yi. (Sela)
5 Mais toi, mon âme, repose-toi paisiblement sur Dieu; car mon attente est en lui.
Ka nemi hutu, ya raina, a wurin Allah kaɗai; dogarata kan zo daga gare shi ne.
6 Lui seul est mon rocher et mon salut, ma haute retraite: je ne serai pas ébranlé.
Shi ne kaɗai dutsena da cetona; shi ne kagarata, ba zan jijjigu ba.
7 Sur Dieu [reposent] mon salut et ma gloire; le rocher de ma force, mon refuge, est en Dieu.
Cetona da girmata sun dangana ga Allah ne, shi ne dutsena mai ƙarfi, mafakata.
8 Peuple, – confiez-vous en lui en tout temps, répandez votre cœur devant lui: Dieu est notre refuge. (Sélah)
Ku dogara a gare shi a duk lokuta, ya mutane; ku faɗi albarkaci bakin zukatanku a gare shi, gama Allah ne mafakarmu. (Sela)
9 Les fils des gens du commun ne sont que vanité, les fils des grands ne sont que mensonge: placés dans la balance, ils montent ensemble plus [légers] que la vanité.
Talakawa dai kamar shaƙar iska suke, Attajirai dai kamar shirim suke; in aka auna a ma’auni, su ba wani abu ba ne; dukansu dai kamar shaƙar iska ne kawai.
10 N’ayez pas confiance dans l’oppression, et ne mettez pas un vain espoir dans la rapine; si les biens augmentent, n’y mettez pas votre cœur.
Kada ku dogara a kan ƙwace ko yin fariya a kayan sata; ko arzikinku ya ƙaru, kada ku sa zuciyarku a kansu.
11 Dieu a parlé une fois; … deux fois j’ai entendu ceci, que la force est à Dieu.
Abu guda Allah ya ce, abubuwa biyu na ji, “Cewa kai, ya Allah, kake mai ƙarfi,
12 Et à toi, Seigneur, est la bonté; car toi tu rends à chacun selon son œuvre.
kuma cewa kai, ya Ubangiji, mai ƙauna ne. Tabbatacce za ka sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya yi.”

< Psaumes 62 >