< Psaumes 56 >

1 Au chef de musique. Sur Jonath-Élem-Rekhokim. De David. Mictam; quand les Philistins le prirent dans Gath. Use de grâce envers moi, ô Dieu! car l’homme voudrait m’engloutir; me faisant la guerre tout le jour, il m’opprime.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
2 Mes ennemis voudraient tout le jour m’engloutir; car il y en a beaucoup qui me font la guerre, avec hauteur.
Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
3 Au jour où je craindrai, je me confierai en toi.
Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
4 En Dieu, je louerai sa parole; en Dieu je me confie: je ne craindrai pas; que me fera la chair?
Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
5 Tout le jour ils tordent mes paroles; toutes leurs pensées sont contre moi en mal.
Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
6 Ils s’assemblent, ils se cachent, ils observent mes pas, car ils guettent mon âme.
Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
7 Échapperont-ils par l’iniquité? Dans ta colère, ô Dieu, précipite les peuples!
Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
8 Tu comptes mes allées et mes venues; mets mes larmes dans tes vaisseaux; ne sont-elles pas dans ton livre?
Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
9 Alors mes ennemis retourneront en arrière, au jour où je crierai; je sais cela, car Dieu est pour moi.
Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
10 En Dieu, je louerai sa parole; en l’Éternel, je louerai sa parole.
Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
11 En Dieu je me confie: je ne craindrai pas; que me fera l’homme?
ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
12 Les vœux que je t’ai faits sont sur moi, ô Dieu! je te rendrai des louanges.
Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
13 Car tu as délivré mon âme de la mort: [ne garderais-tu] pas mes pieds de broncher, pour que je marche devant Dieu dans la lumière des vivants?
Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.

< Psaumes 56 >