< Psaumes 50 >

1 Psaume d’Asaph. Le [Dieu] Fort, Dieu, l’Éternel, a parlé, et a appelé la terre, du soleil levant jusqu’au soleil couchant.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 De Sion, perfection de la beauté, Dieu a fait luire sa splendeur.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Notre Dieu viendra, et il ne se taira point; un feu dévorera devant lui, et autour de lui tourbillonnera la tempête;
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Il appellera les cieux d’en haut, et la terre, pour juger son peuple:
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 Assemblez-moi mes saints, qui ont fait alliance avec moi par [un] sacrifice.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 Et les cieux déclareront sa justice, car Dieu lui-même est juge. (Sélah)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Écoute, mon peuple, et je parlerai; [écoute], Israël, et je témoignerai au milieu de toi. Moi, je suis Dieu, ton Dieu.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Je ne te reprendrai pas à cause de tes sacrifices ou de tes holocaustes, qui ont été continuellement devant moi.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 Je ne prendrai pas de taureau de ta maison, ni de boucs de tes parcs;
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Car tout animal de la forêt est à moi, les bêtes sur mille montagnes.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Je connais tous les oiseaux des montagnes, et ce qui se meut par les champs est à moi.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Si j’avais faim, je ne te le dirais pas; car le monde est à moi, et tout ce qu’il contient.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Mangerais-je la chair des gros taureaux, et boirais-je le sang des boucs?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Sacrifie à Dieu la louange, et acquitte tes vœux envers le Très-haut,
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 Et invoque-moi au jour de la détresse: je te délivrerai, et tu me glorifieras.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Mais Dieu dit au méchant: Qu’as-tu à faire de redire mes statuts, et de prendre mon alliance dans ta bouche?
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Toi qui hais la correction, et qui as jeté mes paroles derrière toi.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Si tu as vu un voleur, tu t’es plu avec lui, et ta portion est avec les adultères;
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Tu livres ta bouche au mal, et ta langue trame la tromperie;
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Tu t’assieds, tu parles contre ton frère, tu diffames le fils de ta mère:
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 Tu as fait ces choses-là, et j’ai gardé le silence; – tu as estimé que j’étais véritablement comme toi; [mais] je t’en reprendrai, et je te les mettrai devant les yeux.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Considérez donc cela, vous qui oubliez Dieu, de peur que je ne déchire, et qu’il n’y ait personne qui délivre.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Celui qui sacrifie la louange me glorifie; et à celui qui règle sa voie je ferai voir le salut de Dieu.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Psaumes 50 >