< Psaumes 29 >

1 Psaume de David. Rendez à l’Éternel, fils des forts, rendez à l’Éternel la gloire et la force!
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Rendez à l’Éternel la gloire de son nom; adorez l’Éternel en sainte magnificence!
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 La voix de l’Éternel est sur les eaux; le Dieu de gloire fait tonner, – l’Éternel sur les grandes eaux.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 La voix de l’Éternel est puissante, la voix de l’Éternel est magnifique.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 La voix de l’Éternel brise les cèdres: l’Éternel brise les cèdres du Liban,
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 Et il les fait bondir comme un veau, le Liban et le Sirion comme un jeune buffle.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 La voix de l’Éternel fait jaillir des sillons de feu.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 La voix de l’Éternel fait trembler le désert; l’Éternel fait trembler le désert de Kadès.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 La voix de l’Éternel fait faonner les biches, et dépouille les forêts; et dans son temple tout dit: Gloire!
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 L’Éternel s’assied sur les flots, l’Éternel s’assied comme roi à toujours.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 L’Éternel donnera force à son peuple, l’Éternel bénira son peuple par la paix.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Psaumes 29 >