< Psaumes 26 >

1 De David. Ô Éternel! juge-moi, car j’ai marché dans mon intégrité, et je me suis confié en l’Éternel: je ne chancellerai pas.
Ta Dawuda. Ka nuna rashin laifina, ya Ubangiji, gama na yi rayuwa marar zargi; Na dogara ga Ubangiji ba tare da kaucewa ba.
2 Sonde-moi, ô Éternel! et éprouve-moi; examine mes reins et mon cœur.
Ka jarraba ni, ya Ubangiji, ka kuma gwada ni, ka bincike zuciyata da tunanina;
3 Car ta bonté est devant mes yeux, et j’ai marché dans ta vérité.
gama ƙaunarka kullum tana a gabana, kuma ina cin gaba da tafiya a cikin gaskiyarka.
4 Je ne me suis pas assis avec des hommes vains, et je ne suis pas allé avec les gens dissimulés;
Ba na zama tare da masu ruɗu, ko in yi tarayya da masu riya;
5 J’ai haï la congrégation de ceux qui font le mal, et je ne m’assiérai pas avec les méchants.
na ƙi jinin taron masu aikata mugunta na ƙi in zauna tare da mugaye.
6 Je laverai mes mains dans l’innocence, et je ferai le tour de ton autel, ô Éternel!
Na wanke hannuwana cikin rashin laifi, ina yawo a bagadenka Ya Ubangiji,
7 Pour entonner la louange, et pour raconter toutes tes merveilles.
ina shelar yabonka da ƙarfi ina faɗin dukan ayyukanka masu banmamaki.
8 Éternel! j’ai aimé l’habitation de ta maison, et le lieu de la demeure de ta gloire.
Ina ƙaunar gidan da kake zama, ya Ubangiji, wurin da ɗaukakarka ke zaune.
9 N’assemble pas mon âme avec les pécheurs, ni ma vie avec les hommes de sang,
Kada ka ɗauke raina tare da masu zunubi raina tare da masu son yin kisankai
10 Dans les mains desquels il y a des crimes, et dont la droite est pleine de présents.
waɗanda akwai mugayen dabaru a hannuwansu, waɗanda hannuwansu na dama suna cike da cin hanci.
11 Mais moi, je marcherai dans mon intégrité. Rachète-moi, et use de grâce envers moi.
Amma na yi rayuwa marar zargi; ka cece ni ka kuma yi mini jinƙai.
12 Mon pied se tient au chemin uni: je bénirai l’Éternel dans les congrégations.
Ƙafafuna suna tsaye daram; cikin taro mai girma zan yabi Ubangiji.

< Psaumes 26 >