< Psaumes 22 >

1 Au chef de musique. Sur Ajéleth-Hashakhar. Psaume de David. Mon Dieu! mon Dieu! pourquoi m’as-tu abandonné, [te tenant] loin de mon salut, – des paroles de mon rugissement?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
2 Mon Dieu! je crie de jour, mais tu ne réponds point; et de nuit, et il n’y a point de repos pour moi.
Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
3 Et toi, tu es saint, toi qui habites [au milieu des] louanges d’Israël.
Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
4 Nos pères se sont confiés en toi; ils se sont confiés, et tu les as délivrés.
A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
5 Ils ont crié vers toi, et ils ont été sauvés; ils se sont confiés en toi, et ils n’ont point été confus.
Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
6 Mais moi, je suis un ver, et non point un homme; l’opprobre des hommes, et le méprisé du peuple.
Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
7 Tous ceux qui me voient se moquent de moi; ils ouvrent la bouche, ils hochent la tête:
Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
8 Il se confie à l’Éternel: qu’il le fasse échapper, qu’il le délivre, car il prend son plaisir en lui!
“Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
9 Mais c’est toi qui m’as tiré du sein [qui m’a porté]; tu m’as donné confiance sur les mamelles de ma mère.
Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
10 C’est à toi que je fus remis dès la matrice; tu es mon Dieu dès le ventre de ma mère.
Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
11 Ne te tiens pas loin de moi, car la détresse est proche, car il n’y a personne qui secoure.
Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
12 Beaucoup de taureaux m’ont environné, des puissants de Basan m’ont entouré;
Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
13 Ils ouvrent leur gueule contre moi, comme un lion déchirant et rugissant.
Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
14 Je suis répandu comme de l’eau, et tous mes os se déjoignent; mon cœur est comme de la cire, il est fondu au-dedans de mes entrailles.
An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
15 Ma vigueur est desséchée comme un têt, et ma langue est attachée à mon palais; et tu m’as mis dans la poussière de la mort.
Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
16 Car des chiens m’ont environné, une assemblée de méchants m’a entouré; ils ont percé mes mains et mes pieds;
Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
17 Je compterais tous mes os. Ils me contemplent, ils me regardent;
Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
18 Ils partagent entre eux mes vêtements, et sur ma robe ils jettent le sort.
Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
19 Et toi, Éternel! ne te tiens pas loin; ma Force! hâte-toi de me secourir.
Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
20 Délivre mon âme de l’épée, mon unique de la patte du chien.
Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
21 Sauve-moi de la gueule du lion. Tu m’as répondu d’entre les cornes des buffles.
Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
22 J’annoncerai ton nom à mes frères, je te louerai au milieu de la congrégation.
Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
23 Vous qui craignez l’Éternel, louez-le; toute la semence de Jacob, glorifiez-le; et révérez-le, vous, toute la semence d’Israël;
Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
24 Car il n’a pas méprisé ni rejeté l’affliction de l’affligé, et n’a point caché sa face de lui; mais, quand il a crié vers lui, il l’a écouté.
Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
25 De toi [vient] ma louange dans la grande congrégation. Je paierai mes vœux devant ceux qui le craignent.
Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
26 Les débonnaires mangeront et seront rassasiés; ceux qui cherchent l’Éternel le loueront; votre cœur vivra à toujours.
Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
27 Tous les bouts de la terre se souviendront, et ils se tourneront vers l’Éternel, et toutes les familles des nations se prosterneront devant toi.
Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
28 Car le royaume est à l’Éternel, et il domine au milieu des nations.
gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
29 Tous les gras de la terre mangeront et se prosterneront: devant lui se courberont tous ceux qui descendent dans la poussière, et celui qui ne peut faire vivre son âme.
Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
30 Une semence le servira; elle sera comptée au Seigneur comme une génération.
Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
31 Ils viendront et raconteront sa justice à un peuple qui naîtra, … qu’il a fait [ces choses].
Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.

< Psaumes 22 >