< Psaumes 18 >

1 Au chef de musique. Du serviteur de l’Éternel, de David, qui adressa à l’Éternel les paroles de ce cantique, le jour où l’Éternel l’eut délivré de la main de tous ses ennemis, et de la main de Saül. Et il dit: Je t’aimerai, ô Éternel, ma force!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
2 Éternel, mon rocher, et mon lieu fort, et celui qui me délivre! Mon Dieu, mon rocher, en qui je me confie, mon bouclier et la corne de mon salut, ma haute retraite!
Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
3 Je crierai à l’Éternel, qui est digne d’être loué, et je serai sauvé de mes ennemis.
Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
4 Les cordeaux de la mort m’ont environné, et les torrents de Bélial m’ont fait peur;
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
5 Les cordeaux du shéol m’ont entouré, les filets de la mort m’ont surpris: (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol h7585)
6 Dans ma détresse j’ai invoqué l’Éternel, et j’ai crié à mon Dieu: de son temple, il a entendu ma voix, et mon cri est parvenu devant lui à ses oreilles.
Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
7 Alors la terre fut ébranlée, et trembla, et les fondements des montagnes furent secoués et furent ébranlés, parce qu’il était irrité.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
8 Une fumée montait de ses narines, et un feu sortant de sa bouche dévorait; des charbons en jaillissaient embrasés.
Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
9 Et il abaissa les cieux, et descendit; et il y avait une obscurité profonde sous ses pieds.
Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
10 Il était monté sur un chérubin, et volait, et il planait sur les ailes du vent.
Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
11 Il mit les ténèbres pour sa demeure secrète comme sa tente autour de lui, des ténèbres d’eaux, d’épaisses nuées de l’air.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
12 De la splendeur qui était devant lui, ses nuées épaisses passaient, de la grêle et des charbons de feu.
daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
13 Et l’Éternel tonna dans les cieux, et le Très-haut fit retentir sa voix, – de la grêle et des charbons de feu.
Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
14 Et il tira ses flèches et dispersa [mes ennemis]; il lança des éclairs et les mit en déroute.
Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
15 Alors les lits des eaux parurent, et les fondements du monde furent mis à découvert, quand tu les tanças, ô Éternel, par le souffle du vent de tes narines.
Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
16 D’en haut il étendit [sa main], il me prit, il me tira des grandes eaux;
Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
17 Il me délivra de mon puissant ennemi et de ceux qui me haïssaient; car ils étaient plus forts que moi.
Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
18 Ils m’avaient surpris au jour de ma calamité, mais l’Éternel fut mon appui.
Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
19 Et il me fit sortir au large, il me délivra, parce qu’il prenait son plaisir en moi.
Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
20 L’Éternel m’a récompensé selon ma justice, il m’a rendu selon la pureté de mes mains;
Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
21 Car j’ai gardé les voies de l’Éternel, et je ne me suis point méchamment détourné de mon Dieu.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
22 Car toutes ses ordonnances ont été devant moi; et ses statuts, je ne les ai pas écartés de moi.
Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
23 Et j’ai été parfait avec lui, et je me suis gardé de mon iniquité.
Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
24 Et l’Éternel m’a rendu selon ma justice, selon la pureté de mes mains devant ses yeux.
Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
25 Avec celui qui use de grâce, tu uses de grâce; avec l’homme parfait, tu te montres parfait;
Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
26 Avec celui qui est pur, tu te montres pur; et avec le pervers, tu es roide.
ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
27 Car toi tu sauveras le peuple affligé, et tu abaisseras les yeux hautains.
Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
28 Car c’est toi qui fais luire ma lampe: l’Éternel, mon Dieu, fait resplendir mes ténèbres.
Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
29 Car, par toi, je courrai au travers d’une troupe, et, par mon Dieu, je franchirai une muraille.
Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
30 Quant à Dieu, sa voie est parfaite; la parole de l’Éternel est affinée; il est un bouclier à tous ceux qui se confient en lui.
Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
31 Car qui est Dieu, hormis l’Éternel, et qui est un rocher, si ce n’est notre Dieu,
Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
32 Le Dieu qui me ceint de force et qui rend ma voie parfaite? –
Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
33 Qui rend mes pieds pareils à ceux des biches, et me fait tenir debout sur mes lieux élevés;
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
34 Qui enseigne mes mains à combattre, et mes bras bandent un arc d’airain.
Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
35 Et tu m’as donné le bouclier de ton salut, et ta droite m’a soutenu, et ta débonnaireté m’a agrandi.
Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
36 Tu as mis au large mes pas sous moi, et les chevilles de mes pieds n’ont pas chancelé.
Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
37 J’ai poursuivi mes ennemis, et je les ai atteints; et je ne m’en suis pas retourné que je ne les aie consumés.
Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
38 Je les ai transpercés, et ils n’ont pu se relever; ils sont tombés sous mes pieds.
Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
39 Et tu m’as ceint de force pour le combat; tu as courbé sous moi ceux qui s’élevaient contre moi.
Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
40 Et tu as fait que mes ennemis m’ont tourné le dos; et ceux qui me haïssaient, je les ai détruits.
Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
41 Ils criaient, et il n’y avait point de sauveur; [ils criaient] à l’Éternel, et il ne leur a pas répondu.
Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
42 Et je les ai brisés menu comme la poussière devant le vent; je les ai jetés loin comme la boue des rues.
Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
43 Tu m’as délivré des débats du peuple; tu m’as établi chef des nations; un peuple que je ne connaissais pas me servira.
Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
44 Dès qu’ils ont entendu de leur oreille, ils m’ont obéi; les fils de l’étranger se sont soumis à moi en dissimulant.
da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
45 Les fils de l’étranger ont dépéri, et ils sont sortis en tremblant de leurs lieux cachés.
Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
46 L’Éternel est vivant; et que mon Rocher soit béni! Et que le Dieu de mon salut soit exalté,
Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
47 Le Dieu qui m’a donné des vengeances, et qui m’a assujetti les peuples,
Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
48 Qui m’a délivré de mes ennemis! Même tu m’as élevé au-dessus de ceux qui s’élèvent contre moi, tu m’as délivré de l’homme violent.
wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
49 C’est pourquoi, Éternel! je te célébrerai parmi les nations, et je chanterai des cantiques à [la gloire de] ton nom.
Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
50 [C’est lui] qui a donné de grandes délivrances à son roi, et qui use de bonté envers son oint, envers David, et envers sa semence, à toujours.
Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.

< Psaumes 18 >