< Psaumes 147 >

1 Louez Jah! car c’est une chose bonne. Chantez les louanges de notre Dieu! car c’est une chose agréable. La louange est bienséante.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 L’Éternel bâtit Jérusalem; il rassemble les exilés d’Israël.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 C’est lui qui guérit ceux qui ont le cœur brisé, et qui bande leurs plaies;
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Qui compte le nombre des étoiles: à elles toutes il donne des noms.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Notre Seigneur est grand et d’une grande puissance; son intelligence est sans bornes.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 L’Éternel affermit les débonnaires; il renverse les méchants jusqu’en terre.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Chantez à l’Éternel avec actions de grâces, psalmodiez sur la harpe à notre Dieu,
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 Qui couvre de nuages les cieux, qui prépare la pluie pour la terre, qui fait germer l’herbe sur les montagnes;
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Qui donne la nourriture au bétail, [et] aux petits du corbeau qui crient.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 Il ne trouve pas son plaisir en la force du cheval, il ne se complaît pas aux jambes de l’homme.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Le plaisir de l’Éternel est en ceux qui le craignent, en ceux qui s’attendent à sa bonté.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Jérusalem, célèbre l’Éternel! Sion, loue ton Dieu!
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 Car il rend fortes les barres de tes portes; il bénit tes fils au milieu de toi;
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 Il met la paix dans tes confins; il te rassasie de la moelle du froment;
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Il envoie ses oracles sur la terre: sa parole court avec vitesse.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 C’est lui qui donne la neige comme de la laine, qui répand la gelée blanche comme de la cendre;
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 Il jette sa glace comme par morceaux: qui peut subsister devant son froid?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 Il envoie sa parole et les fait fondre; il fait souffler son vent: les eaux coulent.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 Il annonce ses paroles à Jacob, ses statuts et ses ordonnances à Israël.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 Il n’a fait ainsi à aucune nation; et ses ordonnances, elles ne les ont pas connues. Louez Jah!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psaumes 147 >