< Psaumes 119 >
1 Bienheureux ceux qui sont intègres dans leur voie, qui marchent dans la loi de l’Éternel.
Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
2 Bienheureux ceux qui gardent ses témoignages, qui le cherchent de tout leur cœur,
Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
3 Qui aussi ne font pas d’iniquité; ils marchent dans ses voies.
Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
4 Tu as commandé tes préceptes pour qu’on les garde soigneusement.
Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
5 Oh, que mes voies soient dressées, pour garder tes statuts!
Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
6 Alors je ne serai pas honteux quand je regarderai à tous tes commandements.
Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
7 Je te célébrerai d’un cœur droit, quand j’aurai appris les ordonnances de ta justice.
Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
8 Je garderai tes statuts; ne me délaisse pas tout à fait.
Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
9 Comment un jeune homme rendra-t-il pure sa voie? Ce sera en y prenant garde selon ta parole.
Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
10 Je t’ai cherché de tout mon cœur; ne me laisse pas m’égarer de tes commandements.
Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
11 J’ai caché ta parole dans mon cœur, afin que je ne pèche pas contre toi.
Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
12 Éternel! tu es béni; enseigne-moi tes statuts.
Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
13 J’ai raconté de mes lèvres toutes les ordonnances de ta bouche.
Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
14 J’ai pris plaisir au chemin de tes témoignages, autant qu’à toutes les richesses.
Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
15 Je méditerai tes préceptes et je regarderai à tes sentiers.
Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
16 Je fais mes délices de tes statuts, je n’oublierai pas ta parole.
Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
17 Fais du bien à ton serviteur, [et] je vivrai et je garderai ta parole.
Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
18 Ouvre mes yeux, et je verrai les merveilles qui sont dans ta loi.
Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
19 Je suis étranger dans le pays; ne me cache pas tes commandements.
Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
20 Mon âme est brisée par l’ardent désir qu’elle a en tout temps pour tes ordonnances.
Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
21 Tu as tancé les orgueilleux, les maudits, qui s’égarent de tes commandements.
Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
22 Roule de dessus moi l’opprobre et le mépris; car je garde tes témoignages.
Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
23 Les princes même se sont assis [et] parlent contre moi; ton serviteur médite tes statuts.
Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
24 Tes témoignages sont aussi mes délices, les hommes de mon conseil.
Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
25 Mon âme est attachée à la poussière; fais-moi vivre selon ta parole.
An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
26 Je [t’]ai déclaré mes voies, et tu m’as répondu; enseigne-moi tes statuts.
Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
27 Fais-moi comprendre la voie de tes préceptes, et je méditerai sur tes merveilles.
Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
28 Mon âme, de tristesse, se fond en larmes; affermis-moi selon ta parole.
Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
29 Éloigne de moi la voie du mensonge, et, dans ta grâce, donne-moi ta loi.
Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
30 J’ai choisi la voie de la fidélité, j’ai placé [devant moi] tes jugements.
Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
31 Je suis attaché à tes témoignages: Éternel! ne me rends point honteux.
Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
32 Je courrai dans la voie de tes commandements, quand tu auras mis mon cœur au large.
Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
33 Éternel! enseigne-moi la voie de tes statuts, et je l’observerai jusqu’à la fin.
Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
34 Donne-moi de l’intelligence, et j’observerai ta loi, et je la garderai de tout mon cœur.
Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
35 Fais-moi marcher dans le chemin de tes commandements, car j’y prends plaisir.
Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
36 Incline mon cœur à tes témoignages, et non point au gain.
Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
37 Détourne mes yeux pour qu’ils ne regardent pas la vanité; fais-moi vivre dans ta voie.
Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
38 Confirme ta parole à ton serviteur, qui est [adonné] à ta crainte.
Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
39 Détourne de moi l’opprobre que je crains; car tes jugements sont bons.
Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
40 Voici, j’ai ardemment désiré tes préceptes; fais-moi vivre dans ta justice.
Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
41 Et que ta bonté vienne à moi, ô Éternel! – ton salut, selon ta parole!
Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
42 Et j’aurai de quoi répondre à celui qui m’outrage; car je me suis confié en ta parole.
sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
43 Et n’ôte pas entièrement de ma bouche la parole de la vérité; car je me suis attendu à tes jugements.
Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
44 Alors je garderai ta loi continuellement, à toujours et à perpétuité;
Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
45 Et je marcherai au large, car j’ai recherché tes préceptes;
Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
46 Et je parlerai de tes témoignages devant des rois, et je ne serai pas honteux;
Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
47 Et je trouverai mes délices en tes commandements que j’ai aimés;
gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
48 Et je lèverai mes mains vers tes commandements que j’ai aimés, et je méditerai tes statuts.
Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
49 Souviens-toi de ta parole à ton serviteur, à laquelle tu as fait que je me suis attendu.
Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
50 C’est ici ma consolation dans mon affliction, que ta parole m’a fait vivre.
Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
51 Les orgueilleux se sont moqués de moi excessivement: je n’ai pas dévié de ta loi;
Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
52 Je me suis souvenu de tes ordonnances de jadis, ô Éternel! et je me suis consolé.
Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
53 Une ardente indignation m’a saisi à cause des méchants qui abandonnent ta loi.
Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
54 Tes statuts m’ont été des cantiques, dans la maison de mon pèlerinage.
Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
55 Je me suis souvenu de ton nom pendant la nuit, ô Éternel! et j’ai gardé ta loi.
Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
56 Cela m’est arrivé, car j’ai observé tes préceptes.
Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
57 Ma part, ô Éternel! je l’ai dit, c’est de garder tes paroles.
Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
58 Je t’ai imploré de tout mon cœur: use de grâce envers moi selon ta parole.
Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
59 J’ai pensé à mes voies, et j’ai tourné mes pieds vers tes témoignages.
Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
60 Je me suis hâté, et je n’ai point différé de garder tes commandements.
Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
61 Les cordes des méchants m’ont entouré: je n’ai pas oublié ta loi.
Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
62 Je me lève à minuit pour te célébrer à cause des ordonnances de ta justice.
Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
63 Je suis le compagnon de tous ceux qui te craignent, et de ceux qui gardent tes préceptes.
Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
64 La terre, ô Éternel! est pleine de ta bonté; enseigne-moi tes statuts.
Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
65 Tu as fait du bien à ton serviteur, ô Éternel! selon ta parole.
Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
66 Enseigne-moi le bon sens et la connaissance; car j’ai ajouté foi à tes commandements.
Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
67 Avant que je sois affligé, j’errais; mais maintenant je garde ta parole.
Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
68 Tu es bon et bienfaisant; enseigne-moi tes statuts.
Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
69 Les orgueilleux ont inventé contre moi des mensonges; j’observerai tes préceptes de tout mon cœur.
Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
70 Leur cœur est épaissi comme la graisse; moi, je trouve mes délices en ta loi.
Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
71 Il est bon pour moi que j’aie été affligé, afin que j’apprenne tes statuts.
Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
72 La loi de ta bouche est meilleure pour moi que des milliers [de pièces] d’or et d’argent.
Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
73 Tes mains m’ont fait et façonné; rends-moi intelligent, et j’apprendrai tes commandements.
Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
74 Ceux qui te craignent me verront, et se réjouiront; car je me suis attendu à ta parole.
Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
75 Je sais, ô Éternel! que tes jugements sont justice, et que c’est en fidélité que tu m’as affligé.
Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
76 Que ta bonté, je te prie, soit ma consolation, selon ta parole à ton serviteur.
Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
77 Que tes compassions viennent sur moi, et je vivrai; car ta loi fait mes délices.
Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
78 Que les orgueilleux soient couverts de honte, car sans cause ils ont agi perversement envers moi; moi, je médite tes préceptes.
Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
79 Que ceux qui te craignent se tournent vers moi, et ceux qui connaissent tes témoignages.
Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
80 Que mon cœur soit intègre dans tes statuts, afin que je ne sois pas honteux.
Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
81 Mon âme languit après ton salut; je m’attends à ta parole.
Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
82 Mes yeux languissent après ta parole; et j’ai dit: Quand me consoleras-tu?
Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
83 Car je suis devenu comme une outre mise à la fumée; je n’oublie pas tes statuts.
Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
84 Combien [dureront] les jours de ton serviteur? Quand exécuteras-tu le jugement contre ceux qui me persécutent?
Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
85 Les orgueilleux ont creusé pour moi des fosses, ce qui n’est pas selon ta loi.
Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
86 Tous tes commandements sont fidélité. On me persécute sans cause; aide-moi!
Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
87 Peu s’en est fallu qu’ils ne m’aient consumé sur la terre; mais moi, je n’ai pas abandonné tes préceptes.
Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
88 Selon ta bonté, fais-moi vivre, et je garderai le témoignage de ta bouche.
Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
89 Éternel! ta parole est établie à toujours dans les cieux.
Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
90 Ta fidélité est de génération en génération. Tu as établi la terre, et elle demeure ferme.
Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
91 Selon tes ordonnances, [ces choses] demeurent fermes aujourd’hui; car toutes choses te servent.
Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
92 Si ta loi n’avait fait mes délices, j’aurais péri dans mon affliction.
Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
93 Jamais je n’oublierai tes préceptes, car par eux tu m’as fait vivre.
Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
94 Je suis à toi, sauve-moi; car j’ai recherché tes préceptes.
Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
95 Les méchants m’attendent pour me faire périr; [mais] je suis attentif à tes témoignages.
Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
96 J’ai vu la fin de toute perfection; ton commandement est fort étendu.
Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
97 Combien j’aime ta loi! tout le jour je la médite.
Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
98 Tes commandements m’ont rendu plus sage que mes ennemis, car ils sont toujours avec moi.
Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
99 J’ai plus d’intelligence que tous ceux qui m’enseignent, parce que je médite tes préceptes.
Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
100 J’ai plus de sens que les anciens, parce que j’observe tes préceptes.
Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
101 J’ai gardé mes pieds de toute mauvaise voie, afin que je garde ta parole.
Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
102 Je ne me suis pas détourné de tes ordonnances, car c’est toi qui m’as instruit.
Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
103 Que tes paroles ont été douces à mon palais, plus que le miel à ma bouche!
Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
104 Par tes préceptes je suis devenu intelligent; c’est pourquoi je hais toute voie de mensonge.
Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
105 Ta parole est une lampe à mon pied, et une lumière à mon sentier.
Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
106 J’ai juré, et je le tiendrai, de garder les ordonnances de ta justice.
Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
107 Je suis extrêmement affligé, ô Éternel! fais-moi vivre selon ta parole!
Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
108 Agrée, je te prie, ô Éternel! les offrandes volontaires de ma bouche, et enseigne-moi tes ordonnances.
Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
109 Ma vie est continuellement dans ma main, mais je n’oublie pas ta loi.
Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
110 Les méchants m’ont tendu un piège; mais je ne me suis pas égaré de tes préceptes.
Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
111 Tes témoignages me sont un héritage à toujours; car ils sont la joie de mon cœur.
Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
112 J’ai incliné mon cœur à pratiquer tes statuts, à toujours, jusqu’à la fin.
Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
113 J’ai eu en haine ceux qui sont doubles de cœur, mais j’aime ta loi.
Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
114 Tu es mon asile et mon bouclier; je me suis attendu à ta parole.
Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
115 Retirez-vous de moi, vous qui faites le mal, et j’observerai les commandements de mon Dieu.
Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
116 Soutiens-moi selon ta parole, et je vivrai; et ne me laisse pas être confus en mon espérance.
Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
117 Soutiens-moi, et je serai sauvé, et je regarderai continuellement tes statuts.
Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
118 Tu as rejeté tous ceux qui s’égarent de tes statuts; car leur tromperie n’est que mensonge.
Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
119 Tu ôtes tous les méchants de la terre, comme des scories; c’est pourquoi j’aime tes témoignages.
Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
120 Ma chair frissonne de la frayeur que j’ai de toi, et j’ai craint à cause de tes jugements.
Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
121 J’ai pratiqué le jugement et la justice; ne m’abandonne pas à mes oppresseurs.
Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
122 Sois le garant de ton serviteur pour [son] bien; que les orgueilleux ne m’oppriment pas.
Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
123 Mes yeux languissent après ton salut et la parole de ta justice.
Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
124 Agis envers ton serviteur selon ta bonté, et enseigne-moi tes statuts.
Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
125 Je suis ton serviteur; rends-moi intelligent, et je connaîtrai tes témoignages.
Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
126 Il est temps que l’Éternel agisse: ils ont annulé ta loi.
Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
127 C’est pourquoi j’aime tes commandements plus que l’or, et que l’or épuré.
Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
128 C’est pourquoi j’estime droits tous [tes] préceptes, à l’égard de toutes choses; je hais toute voie de mensonge.
saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
129 Tes témoignages sont merveilleux; c’est pourquoi mon âme les observe.
Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
130 L’entrée de tes paroles illumine, donnant de l’intelligence aux simples.
Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
131 J’ai ouvert ma bouche, et j’ai soupiré; car j’ai un ardent désir de tes commandements.
Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
132 Tourne-toi vers moi et use de grâce envers moi, selon ta coutume envers ceux qui aiment ton nom.
Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
133 Affermis mes pas dans ta parole, et qu’aucune iniquité ne domine en moi.
Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
134 Rachète-moi de l’oppression de l’homme, et je garderai tes préceptes.
Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
135 Fais luire ta face sur ton serviteur, et enseigne-moi tes statuts.
Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
136 Des ruisseaux d’eau coulent de mes yeux, parce qu’on ne garde pas ta loi.
Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
137 Tu es juste, ô Éternel! et droit dans tes jugements.
Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
138 Tu as commandé la justice de tes témoignages, et la fidélité, strictement.
Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
139 Mon zèle m’a dévoré; car mes oppresseurs ont oublié tes paroles.
Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
140 Ta parole est bien affinée, et ton serviteur l’aime.
An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
141 Je suis petit et méprisé; je n’ai pas oublié tes préceptes.
Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
142 Ta justice est une justice à toujours, et ta loi est vérité.
Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
143 La détresse et l’angoisse m’avaient atteint; tes commandements sont mes délices.
Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
144 La justice de tes témoignages est à toujours; donne-moi de l’intelligence, et je vivrai.
Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
145 J’ai crié de tout mon cœur; réponds-moi, Éternel! j’observerai tes statuts.
Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
146 Je t’invoque: sauve-moi! et je garderai tes témoignages.
Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
147 J’ai devancé le crépuscule, et j’ai crié; je me suis attendu à ta parole.
Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
148 Mes yeux ont devancé les veilles de la nuit pour méditer ta parole.
Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
149 Écoute ma voix, selon ta bonté, ô Éternel! Fais-moi vivre selon ton ordonnance.
Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
150 Ceux qui poursuivent la méchanceté se sont approchés de moi; ils s’éloignent de ta loi.
Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
151 Éternel! tu es proche; et tous tes commandements sont vérité.
Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
152 Dès longtemps j’ai connu, d’après tes témoignages, que tu les as fondés pour toujours.
Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
153 Vois mon affliction, et délivre-moi! Car je n’ai pas oublié ta loi.
Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
154 Prends en main ma cause, et rachète-moi! Fais-moi vivre selon ta parole.
Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
155 Le salut est loin des méchants, car ils ne recherchent pas tes statuts.
Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
156 Tes compassions sont en grand nombre, ô Éternel! – fais-moi vivre selon tes ordonnances.
Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
157 Mes persécuteurs et mes oppresseurs sont en grand nombre; je n’ai point dévié de tes témoignages.
Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
158 J’ai vu les perfides, et j’en ai eu horreur, parce qu’ils ne gardaient pas ta parole.
Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
159 Considère que j’ai aimé tes préceptes; Éternel! fais-moi vivre selon ta bonté.
Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
160 La somme de ta parole est [la] vérité, et toute ordonnance de ta justice est pour toujours.
Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
161 Des princes m’ont persécuté sans cause; mais mon cœur a eu peur de ta parole.
Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
162 J’ai de la joie en ta parole, comme un [homme] qui trouve un grand butin.
Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
163 Je hais, et j’ai en horreur le mensonge; j’aime ta loi.
Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
164 Sept fois le jour je te loue, à cause des ordonnances de ta justice.
Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
165 Grande est la paix de ceux qui aiment ta loi; et pour eux il n’y a pas de chute.
Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
166 J’ai espéré en ton salut, ô Éternel! et j’ai pratiqué tes commandements.
Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
167 Mon âme a gardé tes témoignages, et je les aime beaucoup.
Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
168 J’ai gardé tes préceptes et tes témoignages; car toutes mes voies sont devant toi.
Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
169 Que mon cri parvienne devant toi, ô Éternel! Rends-moi intelligent, selon ta parole!
Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
170 Que ma supplication vienne devant toi; délivre-moi selon ta parole!
Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
171 Mes lèvres publieront [ta] louange, quand tu m’auras enseigné tes statuts.
Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
172 Ma langue parlera haut de ta parole; car tous tes commandements sont justice.
Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
173 Ta main me sera pour secours, car j’ai choisi tes préceptes.
Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
174 J’ai ardemment désiré ton salut, ô Éternel! et ta loi est mes délices.
Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
175 Que mon âme vive, et elle te louera; et fais que tes ordonnances me soient en aide!
Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
176 J’ai erré comme une brebis qui périt: cherche ton serviteur, car je n’ai pas oublié tes commandements.
Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.