< Psaumes 107 >

1 Célébrez l’Éternel! Car il est bon; car sa bonté demeure à toujours.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Que les rachetés de l’Éternel le disent, ceux qu’il a rachetés de la main de l’oppresseur,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Et qu’il a rassemblés des pays, du levant et du couchant, du nord et de la mer.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Ils errèrent par le désert, dans un chemin solitaire; ils ne trouvèrent pas de ville pour y habiter;
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Ils étaient affamés et altérés, leur âme défaillait en eux.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Alors ils crièrent à l’Éternel dans leur détresse, [et] il les délivra de leurs angoisses,
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Et les conduisit dans un chemin droit, pour aller dans une ville habitable.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Qu’ils célèbrent l’Éternel pour sa bonté, et pour ses merveilles envers les fils des hommes!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Car il a rassasié l’âme altérée, et a rempli de biens l’âme affamée.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Ceux qui habitent dans les ténèbres et dans l’ombre de la mort, liés d’affliction et de fers,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Parce qu’ils se sont rebellés contre les paroles de Dieu, et ont méprisé le conseil du Très-haut…
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Et il a humilié leur cœur par le travail; ils ont trébuché, sans qu’il y ait personne qui les secoure.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Alors ils crièrent à l’Éternel dans leur détresse, [et] il les délivra de leurs angoisses:
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Il les fit sortir des ténèbres et de l’ombre de la mort, et rompit leurs liens.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Qu’ils célèbrent l’Éternel pour sa bonté, et pour ses merveilles envers les fils des hommes!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Car il a brisé les portes d’airain, et a mis en pièces les barres de fer.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Les insensés, à cause de la voie de leur transgression, et à cause de leurs iniquités, sont affligés;
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Leur âme abhorre toute nourriture, et ils touchent aux portes de la mort.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Alors ils ont crié à l’Éternel dans leur détresse, [et] il les a délivrés de leurs angoisses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Il a envoyé sa parole et les a guéris, et les a retirés de leurs fosses.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Qu’ils célèbrent l’Éternel pour sa bonté, et pour ses merveilles envers les fils des hommes,
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Et qu’ils sacrifient des sacrifices d’actions de grâces, et qu’ils racontent ses œuvres avec des chants de joie!
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Ceux qui descendent sur la mer dans des navires, qui font [leur] travail sur les grandes eaux,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Ceux-là voient les œuvres de l’Éternel, et ses merveilles dans les [eaux] profondes.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Il a commandé, et a fait venir un vent de tempête, qui souleva ses flots:
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Ils montent aux cieux, ils descendent aux abîmes: leur âme se fond de détresse;
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Ils tournent et chancellent comme un homme ivre, et toute leur sagesse est venue à néant…
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Alors ils ont crié à l’Éternel dans leur détresse, et il les a fait sortir de leurs angoisses;
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Il arrête la tempête, [la changeant] en calme, et les flots se taisent,
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Et ils se réjouissent de ce que les [eaux] sont apaisées, et il les conduit au port qu’ils désiraient.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Qu’ils célèbrent l’Éternel pour sa bonté, et pour ses merveilles envers les fils des hommes;
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Et qu’ils l’exaltent dans la congrégation du peuple, et le louent dans l’assemblée des anciens!
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Il change les fleuves en désert, et les sources d’eaux en sol aride,
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 La terre fertile en terre salée, à cause de l’iniquité de ceux qui y habitent.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Il change le désert en un étang d’eau, et la terre aride en des sources d’eaux;
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Et il y fait habiter les affamés; et ils y établissent des villes habitables,
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Et sèment les champs, et plantent des vignes, qui leur rapportent du fruit.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Et il les bénit, et ils se multiplient beaucoup; et il ne laisse pas diminuer leur bétail; …
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Et ils diminuent, et sont accablés par l’oppression, le malheur, et le chagrin.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Il verse le mépris sur les nobles, et les fait errer dans un désert où il n’y a pas de chemin;
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Mais il relève le pauvre de l’affliction, et donne des familles comme des troupeaux.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Les hommes droits le verront et s’en réjouiront; et toute iniquité fermera sa bouche.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Qui est sage prendra garde à ces choses, et comprendra les bontés de l’Éternel.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psaumes 107 >