< Proverbes 1 >

1 Proverbes de Salomon, fils de David, roi d’Israël,
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 pour connaître la sagesse et l’instruction, pour discerner les paroles d’intelligence;
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 pour recevoir instruction dans la sagesse, la justice, le juste jugement, et la droiture;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 pour donner aux simples de la prudence, au jeune homme de la connaissance et de la réflexion.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Le sage écoutera, et croîtra en science, et l’intelligent acquerra du sens
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 pour comprendre un proverbe et une allégorie, les paroles des sages et leurs énigmes.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 La crainte de l’Éternel est le commencement de la connaissance; les fous méprisent la sagesse et l’instruction.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Écoute, mon fils, l’instruction de ton père, et n’abandonne pas l’enseignement de ta mère;
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 car ce sera une guirlande de grâce à ta tête, et des colliers à ton cou.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Mon fils, si les pécheurs cherchent à te séduire, n’y acquiesce pas.
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 S’ils disent: Viens avec nous, nous serons aux embûches pour le sang, nous nous cacherons pour [guetter] l’innocent, sans cause;
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 nous les engloutirons vivants, comme le shéol, et tout entiers comme ceux qui descendent dans la fosse; (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 nous trouverons toute sorte de biens précieux, nous remplirons nos maisons de butin;
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 prends ton lot parmi nous, il n’y aura qu’une bourse pour nous tous:
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 mon fils, ne fais pas route avec eux, retiens ton pied de leur sentier;
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 car leurs pieds courent au mal, et ils se hâtent pour verser le sang.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Car en vain le filet est étendu devant les yeux de tout ce qui a des ailes;
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 et eux, ils sont aux embûches contre leur propre sang, ils se cachent pour [guetter] leurs propres âmes.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Telles sont les voies de tout homme qui cherche le gain déshonnête, lequel ôte la vie à ceux qui le possèdent.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 La sagesse crie au-dehors, elle fait retentir sa voix sur les places;
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 elle crie à l’entrée des lieux bruyants, aux ouvertures des portes; elle prononce ses paroles dans la ville:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 Simples, jusques à quand aimerez-vous la simplicité, et [jusques à quand] les moqueurs prendront-ils plaisir à la moquerie, et les sots haïront-ils la connaissance?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Revenez à ma répréhension; voici, je ferai couler pour vous mon esprit, je vous ferai savoir mes paroles.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Parce que j’ai crié et que vous avez refusé [d’écouter], parce que j’ai étendu ma main et que personne n’a pris garde,
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 et que vous avez rejeté tout mon conseil et que vous n’avez pas voulu de ma répréhension,
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 moi aussi je rirai lors de votre calamité, je me moquerai quand viendra votre frayeur,
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 quand votre frayeur viendra comme une subite destruction et que votre calamité arrivera comme un tourbillon, quand la détresse et l’angoisse viendront sur vous:
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 alors ils crieront vers moi, et je ne répondrai pas; ils me chercheront de bonne heure, mais ils ne me trouveront point.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Parce qu’ils ont haï la connaissance et qu’ils n’ont pas choisi la crainte de l’Éternel,
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 qu’ils n’ont point voulu de mon conseil, qu’ils ont méprisé toute ma répréhension,
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 ils mangeront du fruit de leur voie et seront rassasiés de leurs propres conseils.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Car la révolte des simples les tue, et la prospérité des sots les fait périr.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 Mais celui qui m’écoute habitera en sécurité et sera tranquille, sans crainte du mal.
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Proverbes 1 >