< Proverbes 8 >

1 La sagesse ne crie-t-elle pas, et l’intelligence ne fait-elle pas retentir sa voix?
Hikima ba ta yin kira ne? Fahimi ba ya tā da muryarsa ne?
2 Au sommet des hauteurs, sur le chemin, aux carrefours, elle se tient debout.
A ƙwanƙoli a kan hanya, inda hanyoyi suka haɗu, ta ɗauki matsayinta;
3 À côté des portes, à l’entrée de la ville, là où l’on passe pour entrer, elle crie:
kusa da ƙofofin shiga cikin birni, a mashigai, ta tā da murya,
4 À vous, hommes, je crie, et ma voix [s’adresse] aux fils des hommes!
“Gare ku, ya mutane, nake kira; na tā da muryata ga dukan’yan adam.
5 Vous, simples, comprenez la prudence, et vous, sots, comprenez ce qu’est le sens.
Ku da kuke marasa azanci, ku yi hankali; ku da kuke wawaye, ku nemi fahimi.
6 Écoutez, car je dirai des choses excellentes, et l’ouverture de mes lèvres [prononcera] des choses droites;
Ku saurara, gama ina da abubuwa masu darajan da zan faɗa; na buɗe leɓunana don in faɗa abin da yake daidai.
7 car mon palais méditera la vérité, et la méchanceté sera une abomination pour mes lèvres.
Bakina yana magana abin da yake gaskiya, gama leɓunana sun ƙi mugunta.
8 Toutes les paroles de ma bouche sont selon la justice, il n’y a rien en elles de pervers ni de tortueux;
Dukan kalmomin bakina suna da adalci; babu waninsu da ya karkace ko kuwa ƙarya ne.
9 elles sont toutes claires pour celui qui a de l’intelligence, et droites pour ceux qui ont trouvé la connaissance.
Ga mai tunani dukansu daidai ne; ba su da laifi ga waɗanda suke da sani.
10 Recevez mon instruction, et non pas de l’argent, et la connaissance plutôt que l’or fin choisi;
Ku zaɓi umarnina a maimakon azurfa, sani a maimakon zinariya zalla,
11 car la sagesse est meilleure que les rubis, et rien de ce qui fait nos délices ne l’égale.
gama hikima ta fi lu’ulu’ai daraja, kuma ba abin da kake sha’awa da za a kwatanta da ita.
12 Moi, la sagesse, je demeure avec la prudence, et je trouve la connaissance [qui vient] de la réflexion.
“Ni, hikima, ina zama tare da hankali; ina da sani da iya rarrabewa.
13 La crainte de l’Éternel, c’est de haïr le mal. Je hais l’orgueil et la hauteur, et la voie d’iniquité, et la bouche perverse.
Jin tsoron Ubangiji shi ne ƙin mugunta; ina ƙin girman kai da fariya, halin mugunta da kuma muguwar magana.
14 À moi le conseil et le savoir-faire; je suis l’intelligence; à moi la force.
Shawara da yin tunani mai kyau nawa ne; ina da fahimi da kuma iko.
15 Par moi les rois règnent, et les princes statuent la justice.
Ta wurina sarakuna suke mulki masu mulki kuma suke yin dokokin da suke da adalci;
16 Par moi les chefs dominent, et les nobles, tous les juges de la terre.
ta wurina sarakuna suke mulki, da kuma dukan manyan mutanen da suke mulkin duniya.
17 J’aime ceux qui m’aiment; et ceux qui me recherchent me trouveront.
Ina ƙaunar waɗanda suke ƙaunata, kuma waɗanda suke nemana sukan same ni.
18 Avec moi sont les richesses et les honneurs, les biens éclatants et la justice.
Tare da ni akwai wadata da girmamawa, dukiya da wadata masu dawwama.
19 Mon fruit est meilleur que l’or fin, même que l’or pur; et mon revenu [meilleur] que l’argent choisi.
’Ya’yan itacena sun fi zinariya zalla; amfanin gonar da nake bayar ya fi azurfa mafi kyau.
20 Je marche dans le chemin de la justice, au milieu des sentiers de juste jugement,
Ina tafiya a hanyar adalci, a kan hanyoyin gaskiya,
21 pour faire hériter les biens réels à ceux qui m’aiment, et pour remplir leurs trésors.
ina ba da wadata ga waɗanda suke ƙaunata ina sa wuraren ajiyarsu su cika.
22 L’Éternel m’a possédée au commencement de sa voie, avant ses œuvres d’ancienneté.
“Ubangiji ya kawo ni a matsayi na farko na ayyukansa, kafin ayyukansa na tuntuni;
23 Dès l’éternité je fus établie, dès le commencement, dès avant les origines de la terre.
an naɗa ni tun fil azal, daga farko, kafin duniya ta kasance.
24 Quand il n’y avait pas d’abîmes, j’ai été enfantée, quand il n’y avait pas de sources pleines d’eaux.
Sa’ad da babu tekuna, aka haife ni, sa’ad da babu maɓulɓulai masu ruwa;
25 Avant que les montagnes soient établies sur leurs bases, avant les collines, j’ai été enfantée,
kafin a kafa duwatsu a wurarensu, kafin tuddai ma, an haife ni,
26 lorsqu’il n’avait pas encore fait la terre et les campagnes, et le commencement de la poussière du monde.
kafin ya yi duniya ko gonaki ko wata ƙurar duniya.
27 Quand il disposait les cieux, j’étais là; quand il ordonnait le cercle qui circonscrit la face de l’abîme,
Ina nan sa’ad da ya kafa sammai a wurarensu, sa’ad da ya shata sararin sama a kan fuskar zurfafa,
28 quand il établissait les nuées en haut, quand il affermissait les sources des abîmes,
sa’ad da ya kafa gizagizai a bisa ya kuma kafa maɓulɓulan zurfafa daram,
29 quand il imposait son décret à la mer, afin que les eaux n’outrepassent point son commandement, quand il décrétait les fondements de la terre:
sa’ad da ya ba wa teku iyakarsa domin kada ruwaye su zarce umarninsa, da kuma sa’ad da ya shata tussan duniya.
30 j’étais alors à côté de lui son nourrisson, j’étais ses délices tous les jours, toujours en joie devant lui,
A lokacin ni ne mai tsara abubuwa a gefensa. Na cika da murna kowace rana, kullum ina farin ciki a gabansa,
31 me réjouissant en la partie habitable de sa terre, et mes délices étaient dans les fils des hommes.
ina farin ciki da dukan duniyarsa ina murna da’yan adam.
32 Maintenant donc, fils, écoutez-moi: bienheureux ceux qui gardent mes voies!
“Yanzu fa,’ya’yana, ku saurare ni; masu albarka ne waɗanda suke kiyaye hanyoyina.
33 Écoutez l’instruction, et soyez sages, et ne la rejetez point.
Ku saurari umarnina ku kuma zama masu hikima; kada ku ƙyale ta.
34 Bienheureux l’homme qui m’écoute, veillant à mes portes tous les jours, gardant les poteaux de mes entrées!
Mai albarka ne wanda ya saurare ni; yana tsaro kullum a ƙofofina, yana jira a ƙofar shigata.
35 Car celui qui m’a trouvée a trouvé la vie, et acquiert faveur de la part de l’Éternel;
Gama duk wanda ya same ni ya sami rai zai kuma sami tagomashi daga Ubangiji.
36 mais celui qui pèche contre moi fait tort à son âme; tous ceux qui me haïssent aiment la mort.
Amma duk wanda ya kāsa samuna ya cuci kansa; dukan waɗanda suke ƙina suna ƙaunar mutuwa ke nan.”

< Proverbes 8 >